a over.
Saida yayi wanka yayi order coffee sannan ya janyo wayar ya shiga nemanta da gaske yayi kewarta ba kadan ba, shifa yana ganin yarinyar Nan itace weakness dinsa duk inda take tana manne a kirjinsa ko barci yake itace a cikin barcin idan ba ganinta yayi ba ko yaji muryar da da akwai damuw, yaga alama any nan gaba ze iya kulla wani abun arziki kuwa? tun yanzu da gishiri bai Sha Kan kazar ba yana jinsa haka Yaya idan labarin ya sauya salo?
Abin mamaki wayar switch off.
Zuru yayi Yana kallon wayar "me kenan?"
Yasan dai ba matsalar charge bane, Sameer ya Kira, duk da basu Dade da Gama waya ba.
Sameer yayi mamakin ganin wani Kiran nasa.
Kafin Sameer ya Kai ga magana Mahmud ya Riga shi.
"Meya faru ne a Asibitin naji wayarta a rufe ko jikin ne ta tashi da akayi Mata gwaje-gwajen?"
"A'a gaskiya normal muka dawo har muka biya nan Murtala Muhammad way sukayi sayayya Kasan Rukayya bataso a zauna lafiya,idan tajita da kudi ba zaman lafiya. Dan Allah ka daina turo mata kudi har madam tabar garin nan, kasan Ruky da yawo Kullum aka fita saita qirqiro zuwa wani gurin, wani Abun ne ya faru yanzun ?"
"A'a ba komai, kada ka manta da maganar kayan da za'a sauke gobe a Nan kanon a turasu can Azaren munyi magana da Habib dazu".
"Ok in Sha Allah".
Sukayi sallama, ji yayi baze iya fada masa komai ba. Wayar ya aje kusa dashi wani tunani yayi sai yaji dariya ta kubce masa "zakiyi bayani da yaren garinku yarinya duk yanda akayi taji wata maganar yanzu a Asibitin yasan Haseena farin sani yanda yaji ta damu da sanin relationship din dake tsakanin sa da zahra yasan zatayi duk yanda zatayi ta shigo da wata maganar wadda zatayi touching dinta tunda shekarun da wayonsu ba Daya bane.
Itama Zahra kasa cin komai tayi fridge ta bude ta saka ice cream din da chocolates tayi kwanciyar ta bayan tayi Addu'a, amma barcin Kuma yace baisan zancen ba, tashi tayi zaune a tsakiyar gadon tana tariyo rayuwarta ta baya "ko yaushe Zan Zama stable a rayuwata? sai hawaye suka zubo Mata "Ubangji ka hanani ganin bakin cikin gidan Aure, lamarin Yana neman yafi karfina ka jibinci lamurana Dan isar fiyayyan halitta Annabin Rahama Muhammad s a w.w.
Bansan ko waye ba wannan bawan naka, kafini saninsa ka amintar Dani a cikin lamarinsa daka barni na tozarta, ka kareni daga dariyar makiyana Ubangiji kasan ko suwaye suke mini yankan Bata a cikin lamarina, kayi min kariya ka bani juriyar abinda ka jarrabeni dashi kasa ya zamar min kaffara.
Tasa tafin hannunta a fuskarta taAUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH.
Page 40.
______ karfe takwas saura Zahra ta fito cikin shigarsu ta asali doguwar Riga baka Mai aikin zare maroon sai kananan stones har kasa,tayi rolling da maroon din veil, cikin takunta na rausaya take gannaro steps din, tana baza sansanyan kamshi, ba kowa a parlourn sai wani sanyi da kamshin freshners ke tashi, Dan Jim tayi tana tunanin ta koma kota zauna sai Kuma ta jiyo alamun motsin kwanuka a kitchen gurin da taga suna shiga ta nufa tunda ba sanin Kan gidan tayi ba, tunda ta shigo iyakarta Nan sai Kuma bedroom din da take, tana dosar gurin wani kamshin girki yayi Mata sallama, babban kitchen ne na zamani Mai kunshe da na'urori birjik kamar a wani babban Hotel ko irin modern restaurant din nan iya Rahane ta gani tana yanka wani Abu yayin da zilai ke tsaye tana duba wani abu a tukunya.
Sallama tayi musu tana fadin "Ina kwanan ku".
A tare suka juyo suna amsawa tare da fadin "ya Kika kwana da jikin?".
Dan juya Kai tayi tana fadin. "Nifa Babu abinda ke damuna kawai dai Dan a dunga yawo ne da Bata lokaci, wallahi har kunya nake ji" .
"A kul Kika Kara fadar haka tunda mijinki yace Kizo a duba aga menene matsalarki kada ki watsa Masa qasa a Ido ki sage Masa gwiwa akan kokarinsa, kije idan Allah yasa Babu komai shike Nan idan Kuma anga abinda ke kawo ciwon a magance shi".
"Wannan gaskiya ne".
Zilai ta fada tana sauke girkin.
"To in Sha Allah na daina iya".
"Yauwa kokefa fa ai idan Kika Fara da haka ko lalular da tafi haka baze Maida hankalinsa ba duk da ba fata ake ba".
"Dan Allah Aunty zilai bani wayarki na Kira Ammah tawa tun jiya ta kashe kanta taki kunnuwa".
Ta fada tana istigifari a zuciyar ta Dan tasan karya ta shara.
" To Bari na dauko Miki tana can a daki"
Ta wanke hannunta ta nufi kafar fita Zahrar tana biye da ita, sai da suka fito zilan ta kalli Zahra "uwar dakina Dan Allah Wai Kinga kuwa dakin da aka ajeni a ciki Dan Allah muje kiga wannan duniyar da aka sakani kamar dakin gidanki,to acan dai bana Hawa gadon Amma wannan akai na kwana har naso in makara Allah yasa ita Iya Rahane Bata makara ba".
Dariya Zahra tayi tana fadin "daina fada Aunty zilai sai a Raina mu wallahi, muje Naga dakin naki Daman ban San inda kike ba Koda tsoro ze kamani sai nayo gudun hijira".
A parlour na biyu suka shiga wani corridor bazaka taba cewa da dakuna a gurin ba steps ne kamar goma suka haura sama Nan ma wani parlourn ne da two three bedrooms biyu suna kallon juna sai Daya daga gefe.
"Masha Allah" Zahra ke fada a zuciyar