iga dakin da Hajiyar.
*******
A qalla sun dauki minti kusan Sha biyar kafin Zahra ta Gama. Parlour na biyu Rukayyar taja Zahra suka shiga Bai Kai na farkon girma ba Amma ba karya Shima ya hadu kamar jira ake su zauna wayar zahrar ta dauki sansanyan kidan ringtone din ta.
"Amma"
Ta fada tana picking din Kiran sallamar Ammar ta amsa tana fadin "kiyi hakuri Ammah wallahi yanzu na fito daga wanka naci abinci, yanzu nake son kiranki na fada Miki mun sauka lafiya".
Daga can Ammar ta amsa Mata da "babu komai da fatan dai komai lafiya ba wata damuwa? zilai ce taso daga min hankali Wai wani gida aka kawo ku gari guda bata taba shiga ko kwatankwacin irinsa ba kamar Kuna wata kasar ita tsoro takeji".
Dariya sosai zahra tayi Jin yanda zilai ta nadi zance ta fesawa Ammah.
"Kai haba Ammah kyale Aunty zilai rudunta ne kawai, gidan Dan babba Kam babba ne Amma komai normal Ina Jin gidan wani friend din oga Sameer ne aka kawo mu, Kuma momin su oga Sameer ma Saida ta turo Mai aikinta daya da kanwarsa daya Aunty Rukayya gata ma nuna tare ku gaisa".
Wayar zahrar ta mikawa Rukayya suka gaisa da Amma, godiya Ammar ta dinga yiwa Rukayyar har kunya ta kamata tace Kuma ta bawa Zahra number din mommy ta kirata tayi Mata godiya.
Sallama sukayi da Ammar suna kashewa Kiran ya shigo international tana gani tasan shine.
Dagawa tayi tana masa sallama Jin muryarta ba kamar jiya ba ya sauke ajiyar zuciya a hankali da Bai yarda ba da Sameer ya fada masa kamar batayi ciwo ba sai yanzu da yaji muryarta tana fita ba kamar jiya ba.
Sallamar ya amsa Yana fadin "my previous...".
Wani deeply saida tsikar jikinta ta bada wani yarrr. "Wash" ta fada.
Kara Kiran sunan yayi a hankali ciki wata murya Mai tada zaune tsaye "me ya faru ne to jikin ne"?".
"A'a ba komai" ta fada a shagwabe.
Rukayya na ganin haka ta Miki tana nuna Mata tana zuwa Dan ta barta ta sake yanda ya kamata.
"Alhamdulillahi haka nake son ji, ya ciwon ya daina ko yanayi kadan kadan".
"Ya M na warke yanzu ba wani Abu da yake damuna dama mu koma gida kawai tunda ya wuce, kawai naje Naga baby muje mu gaishe da mommy da Umman sajida zuwa jibi mu koma, Dan Allah kace to kaji Kuma fa kaga gidan da oga Sameer ya kawo mu gaskiya ka fada Masa ya mayar damu gidansa ko gidan mommy wallahi yayi girma Ni tsoron inda aka kaini nakeyi gurin yayi nisa da main parlour Kuma wani abin mamaki kasan funitures din dake dakin irin na dakinka ne na Azare komai da komai".
Dan Jim yayi kafin yace irin nawa Kuma wace unguwa ya kaiku?".
Dan Jim itama tayi. "Ina ga ko Dawako Road Nasarawa G.R.A.
"Ok nasan gidan na wani friend dinsa ne, wane bedroom din aka Baki?".
" Bangaren dama daga can ciki sosai".
Shiru yayi wato Sameer be bude Mata master bedroom din ba kenan.
"Precious ki hakura a duba min ke kinsan kuwa tension din dana shiga akan ciwon nan naki? kiyi hakuri ayi bincike akai kawai sai nafi samun kwanciyar hankali, gida Kuma nasan shi Baki da matsala dashi Dan cike yake da tsaro ba wata kafa da za'a shigo cikinsa".
"Baka Gane ba nifa ni kadai ce bazan iya kwana a gurin ba sai dai Aunty Rukayya tazo mu kwana".
Ta fada kamar zatayi masa kukan shagwaba.
"A'a ban Amince ki kwana da kowa ba, ba abinda ze kamaki matsoraciya kawai kice na shirya nida nake fatan Allah ya hore min nayi Miki Wanda yafi wannan girma yanda Zaki sake ki walwala keda yaran mu, to kina tsoron wannan ma inaga Wanda nake fatan ajiye sarauniyar Mata a ciki Zahra fa kike ko cikin taurari keta dabance, haka kawai ki janyo min wata ta hanani rawar gaban hantsi da dare so nake ki ragemin zafi idan da wata a dakin ai kin sabautani ko baza'a taimawa dan malam ba?".
Ya fada cikin wata irin kasala wadda ta saka Zahra Jin wani irin Abu a jikinta. "Ya Ilahiy Ajib"
Ta fada cikin kasakalliyar murya.
"Yan Mata yaya dai Kona gudo ne kina bukatata a kusa"
Ya fada Yana huro Mata iskar Bakinsa ta cikin phone din, da sauri ta cire wayar daga kunnanta, Dan da gaske sakon yaje inda aka aike shi kashe Kiran tayi bako sallama.
AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH.
Page 39.
________Wurin karfe takwas Sameer ya shigo gidan, wayar Rukayya ya Kira yace su fito doctor tana jiransu, lokacin suna bedroom din da zahrar take suna cakusawa da Zahra akan wata Rigar shadda 'yar Mali da Rukayyar ta daukowa Zahra cikin kayan da Sameer ya bada ta sawo haka Nan Rukayyar taga zata Dace da zahrar shi yasa ta nace akan ta sakata ita kuma tana ganin tayi Mata girma da yawa, Jin Kiran Sameer yasa ta hakura ta saka sai gashi tayi Mata das kamar an gwadata aka Dinka.
Shar ta fito kamar ka dauke ka buye saboda kyau sai yarintarta ta Kara fitowa, dauri mai kyau Rukayya tayi Mata tunda ta kware har makeup din amare takeyi, light makeup tayi a fuskar ta sai ta fito kamar amarya ranar a yini.
"Masha Allah" kadai Rukayya ke fada ba karya kyau daban yake ko ita mace zahra ta tafi da imaninta to yayi namiji Kuma? Bata yarda da kyau idan yayi yawa hadari bane sai yanzu da Zahra ke gaban ta Dan babu nami