a magantu "To Mama tunda yace taje a duba lafiyar ta ai dole taje tunda da gaske Yana cikin damuwa".
Dan tabe Baki tayi tana fadin. "Ai kam sai kuje nasan dai rabe-rabe zakuyi a gidan uban gidan nasa".
Duk abinda ake Ammah najin su amma ko kallon su batayi ba, haka zilan ma Bata Kara fadin komai ba ta fice daga parlourn.
Hamza ne ya leko parlourn ya gaishe da Ammah tunda sun gaisa da Mama, Zahra ta gaishe shi Ya amsa yana fadin "ya jikin naki? Ku fito inji Abba zaku wuce kanon".
Ta amsa da "to Yaya, jikin da sauki nafa ware wlh, kawai dai".
"To Allah ya Kara lafiya".
Ya juya ya koma.
Zilai ce ta shigo da sauri tana "Ammah zamu tafi ayi Mana addu'a".
Dan murmushi tayi "Allah ya tsare ya bada lafiya".
"Allahumma Amin".
Gurin Ammah Zahra ta karaso a hankali ta rungumeta kamar zatayi kuka, zamu tafi Ammah saina Kira idan munje kada ki Kira Aunty Hasana tunda Bata Dade da tafiya ba, Allah yasa ma gobe zamu juyo gida wallahi bana son zuwa nifa".
Bayan ta Ammah ta Dan shafa tana fadin "kuje ba komai In Sha Allah za'a dace a gano menene matsalar tunda suna da Qualified Gynecologist doctors, Allah ya tsare hanya".
Kai ta gyadawa Ammar ta saketa ta koma ta dauki hand bag dinta sai lokacin tayiwa Mama kallon Ido cikin Ido.
Zamu tafi Mama sai Allah ya dawo damu". Tayi gaba tana rike da hannun Musaddiq sukayi waje, Bata bi takan abinda mamar ke fada ba, da sauri mamar ta rufa musu baya ko sallama batayiwa Ammah ba, wani lokacin Ammah tana mamakin yanda Mama ke nuna tsana da hassada akan Zahra idan abin ya taso Mata Bata iya hiding dinsa dole saita nuna an gane.
"Allah ya raba na gari da mugu li'ilafi quash".
Ammar ta fada tana komawa kitchen inda take kokarin hadawa Abba break fast.
Zahra na rike da hannun Musaddiq suka fito compound din.
Mama na fitowa sukayi kicibus da sahura da sauri ta kyara Mata tabi Zahra a baya, ta nufi part dinta ita Kuma sahurar tabi Zahra da sauri.
Ganin Abba a harabar gidan ya hana sahura garasowa gurin zahrar dole taci burki a gefen second gate din. Zahra gurin Abban ta nufa Yana ganota ya Fara fadar "Masha Allah! Uwata jikin yayi kyau, ya kika kwana?".
"Da sauki Abba, Ina kwana?"
Ta fada tana tsugunnawa kusa dashi.
"Lafiya kalau Aina leka dana dawo daga masallaci akace Baki tashi ba".
"Eh Ammah ta fada min, nifa Abba dama hakuri akayi da zuwan Nan nafa warke ba inda yake min ciwo yanzu".
Sameer ne ya shigo da alama daga wurin Baba Malam yake Dan harda Habib suka shigo, gurin Abba suka nufo Habib ya gaishe da Abban sannan Zahra ta gaishe su shida Sameer din suka dubata, mikewa tayi suka nufi inda Malam Bala direba yake jiran Auta su tafi makaranta, sai ya shiga ya zauna sannan Zahra ta bashi 1k, tace ga kudin chocolate Nan idan ka dawo Ammah zata baka wasu na saka Aunty zulai ta debo maka".
"Nagode Aunty Allah ya sauwaqe Miki Zan Miki addu'a idan nayi sallah, malam Bala ne ya karaso suka gaisa da Zahra ya tada motar suka fice Musaddiq Yana daga Mata hannu.
Ta juyo kenan ta hango zilai da sahura sun nufi gurin su Abba suna gaishe su sannan Habib ya karbi key din motar suka zuba kayan dake hannun su.
Sallama su Sameer sukayiwa Abban suka nufi gurin motar, zahrar ce ta dawo gurin Abban tana fadin "zamu tafi Abbana ayi Mana addu'a"
"Allah ya tsare hanya uwata ya Baki lafiya yasa daga wannan zuwa Asibitin a samu warakar wannan ciwon".
"Amin Abba nagode mun tafi sai nu dawo" ta juya ta nufi motar.
Har gurin motar Abban ya karaso Yana musu Addu'a da fatan sauka lafiya.
A hankali Sameer yayi kwana ya nufi gate din fita Abban Yana daga musu hannu, haka ma Ya Hamza shima Saida yaga ficewarsu sannan ya koma side dinsu, sunzo fita Sameer ya dunkulo kudi yaba Mai gadi cikin murna ya Fara jero Masa Addu'oi da fatan Alkhairi har yayi Dan nisa suna jiyo muryarsa.
A wurin gidan sarki Habib ya sauka, sukayi sallama da Sameer yayiwa zahra sallama da fatan samun lafiya Mai dorewa, yayi gaba zuwa ina zaya.
Sun mika a tafiyar sosai Sameer ya Dan juyo kadan Yana fadin.
"Madam tun jiya nake Kiran wayar ki ba'a dauka".
Dan kwantar da Kai tayi jikin seat din tana fadin. "Wallahi rabona da wayar tun jiya da safe a gida na barta lokacin Ina Zan iya tunawa da wata waya Ina tunanin ko ranar karshen ce tazo, sai dazu da Aunty zilai ta dauko min nabi wasu missed calls din kafin na Kira taka number din ya Hamza ya shigo yace kazo mu fito, na gode kwarai da kulawar ka Allah ya Raya Mana babyn mu". Ta fada tana Dan murmushi.
Shima murmushin yayi tana fadar "wato baby kadai Zaki tambaya Banda mamansa wato saboda sunan mijinki ne son Kai ko?.
Hannunta ta saka ta rufe fuskarta.
Dariya zilai tayi tana fadin tuba muke Yallabai ai baza'a Fara haka ba, gani tayi baby shine bako".
"Kin Kare ta dai kawai Aunty".
Tafiyar awa biyu da minti Arba'in da biyar suka shigo Kano.
Suna area mariri Sameer ya lalubo Rukayya.
"Da fatan komai yayi yanda akeso ya zama ready ko?"
Sauraren amsar da take fada Masa yake, kafin yace "ok mun shigo ki Kira mommy tasa salmanu ya kawo iya Rahane ya