i surukar da zatayi Miki fiye da yanda like min, Wai kin samu yin magana da mutumina kuwa bayan munyi wayar nan?".
"A'a har yanzu be nemi kowa ba ina ganin ko ba lafiya ba dai shirun tayi yawa ya Kamata ace zuwa yanzu yayi hakuri ya huce ya dawo gida".
Ammin ta fada cikin damuwa.
"Ba komai in Sha Allah lfy na fada Miki yanda mukayi da mustapha kema kince kina bibiyarsa ayi ta addu'a Allah ya sassauto da fushinsa ya waiwayo gida wallahi ko cikin dare yaron Nan ya Fadi min a Rai to barcina ya Kare Kullum ta Allah sai anyi mini saukar Alqur'ani akan Allah ya bashi kariya a duk inda yake wallahi nayi Dana sanin fada masa maganar da nayi danasan maganar tawa ze dauketa da zafi wlh da bazan fada masa ba yana cikin zafi".
Hawaye ne ya balle Mata kamar lalataccen famfo har da shashhshekar ta.
"Dan Allah Hajiya kiyi hakuri wlh ba maganar ki bace tasa yabar gida nakin dai yazo Kan gab'a ne kawai".
"A'a keda Baki Nan mukayi yazo Nan Yana ta huci Dan motar dazo a ciki ma ko kashe ta baiyi ba ya fado min Kamar an jefo shi, Yana huci Yana Fadi wlh duk duniya ba Wanda ya Isa yasa ya auri safna Koda Matap sun kare shi Daman koya aureta biyayya ne zeyi Yana da wadda yake da muradin aure, ni kuma a lokacin bani da cikakken masaniyar abinda yake faruwa kinja layin kada a fada min gaskiyar maganar,Ina bude Baki sai ce Masa nayi idan ya ciki shi d'ane na halali ya shiga duniya ya Nemo min yarinyar da yake maganar a kanta Wanda take ganin darajarta tafi ta zuwairiyyar, wlh shiru yayi a inda yake tsaye kasa cemin komai yayi Kusan tsawon minti biyar, kafin ya kalli idona yace min wlh zakiga cikakken Dana halak, ki rubuta ki aje idan kin qara ganina a sokoto ba tare da ita ba to kuwa shege ne ni,idan Kuma ban sameta nida sokoto har abada ya juya ya wuce ko motar Bai kalla ba Kuma tun daga Ranar har Rana Mai kamar ta yau ban Kara saka mahmudu a idona ba, sai dai Babban yaronsa Yana zuwa ganina Yana kawo min duk abinda Mahmudun yake kawo min ciki kuwa harda magungunan da nake sha na hawan jini".
Ammi tayi mamakin Jin Sameer na zuwa gurin Hajiyar koda Wasa Bata taba Jin haka ba, Kenan wato kafa ya bawa mutane Yana cikin Nigeria din kenan bawai inda ake zaton zashi ba.
"Allah kyau Hajiya ki daina damun kanki, jikina Yana bani Yana cikin kasar Nan Kuma Yana da labarin komai tunda kikace min Sameer na zuwa, duk inda yake ya sani ya hana shi ya fada ne kinsan halin kayanki dai".
Mardiyya da Urat Hajiyar ta kalla Tana fadin "yan nema kunki iyayenku sai uwar wasu tun barinki garin Nan yaran Nan suka tare a Nan Wai saina kaisu Yamai gurinki tunda aka fada musu naje suka tada hankalin iyayen sai su dawo Nan idan Zan koma na tafi dasu, Kinga mardiyya jiya da Iyayen sukazo daki ta gudu ta rufe Dan ma kada su tafi da ita, ko makaranta sai dai direban ya biyo ya dauke su anan ya dawo min dasu Nan".
Kansu Ammi ta shafa tana fadin rigima ta kare tunda ga Ammin ku ta dawo ko?".
Kai suka gyada Mata a tare.
Masu aikin Hajiya ne suka shigo ta kofar baya daga kitchen suna fadin "lale marhabin da Ammi barka da zuwa".
Gaisawa sukayi a mutunce tana tambayar su iyalansu.
Abinci na musamman masu aikin suka gabatarwa da Ammi Wanda Hajiya ta hanasu sakat tun safe ake saukewa da dorawa da gaske Babu Mai shafewa Ammi Zane a gurin Hajiya tana sonta kamar me.
Sai bayan insha'i Ammi ta kwashi su Urat ta nufi gida cikin motar data Bari a gidan Hajiyar. So take ta bada mamaki yanda ta fice batare da sanin kowa ba a wayi gari a ganta batare da kowa yasan sanda ta dawo ba, duk gidan amintacciyar Mai aikinta kawai ta Kira ta fada Mata tana Nan Zuwa garin yay ko su Abeeda ba Wanda ta fadawa tasan zumudin su ze saka kowa ya sani.
************
Safa da marwa take tun bayan gama wayarta da Aunty Ladi ranta idan yayi dubi a bace yake Wai shi wannan yaron wane iri ne aiki akeyi a kansa Amma Kamar ana zubawa a teku wannan guri na uku ne da Aunty Ladi taje Mata a Jos Amma amsar daya ce wannan yaron yafi karfinta, Mata ne guda biyu a teaye a kansa da addu'a sannan yana da tsarin jiki na ban mamaki Nan kusa ba abinda zeyi tasiri a kansa sai ikon Allah.
Wayarta ta dauko Asabe ta Kira cikin k"an k'anin lokaci ta daga Kiran "kizo ina jiranki yanzu". Ta kashe wayar tayi wurgi da ita Kan gado.
Cikin abinda bai wuce minti Sha biyar ba Asabe ta shigo gidan ko part din Ammah Bata shiga ba kamar yanda ta Saba direct ta wuce gurin Mama.
Parlourn ba kowa ganin haka yasa ta wuce bedroom dinta a tsaye ta sameta tana kaiwa da kawowa Ido yayi Mata jawur kamar na tsohon mashayi.
Ko sallamar ta Mama Bata ba ta amsa ba ta, fara fadin "Ina ne garin da kikace min 'yar dago kawarki ta fada Miki da wani shahararren mutum Mai aiki kamar yankan wuka?".
Shigowa tayi ta zauna tana kallon mamar "Wai lafiya na ganki haka?"
"Ina fa lafiya! Aunty Ladi ce ta tasheni daga barci take fada min taje har guri uku ba sa'a, Wai yanda suka fada Mata yanzu ne ma Zahra ta gamu da Wanda ake ta fada Mana a baya bawai wadanda mukayi ta aiki a kansu ba, Kuma Shi wannan din duk