MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ga mamakinsu Kawu Auwal ne wato kanin Ma’u tare da Habib din. Suna hada ido Mustapha ya kai masa duka yana cewa ‘Shine zaka fice ba tare da ka gayawa mutane ba saboda raini ko?’
Alhaji yace ‘Ka barshi mana ya zauna yayi bayani.’
Suka karasa cikin gidan suka zauna a parlor din Alhaji.
Bayan sun gaggaisa Kawu Auwalu yace ‘Wallahi nima da asuba Mama ta kirawoni tace na zo na dawo da shi, itama ta yi zaton an san yana gidan shi yasa ma bata nemi kowa ba. Sai dazu bayan sallar asuba Antinsa Khadeeja ta kirawota tana cigiyarsa. Shine ta kirawoni tace na kawo shi nan nayi bayani.’
Alhaji yayi masa godiya sannan ya dubu Habib yace ‘Mutumina ya haka kuma? Me suka yi maka a gidan da zaka bi dare ka gudu? Kuma madadin ka zo ka gaya min sai ka tafi ka dagawa Mama hankali.’
A nan ne ya sami dama ya gayawa Alhaji abinda ya faru, sannan ya sanar da shi irin zaman da ake yi a gidan.
Hajia tace ‘Dama Aminan Jidda ta fada, tace wancan zuwan da suka yi gidan basu ma ga Najan ba. Kamar yaran suna kasa su da mai aiki suna rayuwarsu ita kuma tana sama ita da nata yaran, kuma yanda ya fada haka Aminana ta fada tace shi kanshi Mustaphan yaran basa ganinshi sai dai idan ya sauko.’
Shima Auwalu ya tabbatar musu da cewa duk wadannan maganganu yaran sun dade da yiwa Mama bayani, sai dai da yake ta dauka ba huruminta bane shi yasa ma bata ce komai ba. Amma dai gaskiya da akwai matsala, tunda ai da ba a taba samun matsala irin wannan ba.’
‘Hakane, in sha Allahu za a duba kuma a dauki mataki.’ Alhaji ya fada.
Suka karasa tattaunawa Auwalu yayi musu sallama ya tafi.
Shima Mustapha ya mike ya sa Habib a gaba don su tafi, sai dai shi habib din ya nuna ba zai koma don ya fi so ya zauna a nan wajen Hajia. Alhaji ne ya saka shi a gaba da nasiha yana nuna masa gara ya zauna saboda kannensa, kada ya tafi ya barsu su kuma bai san me zai faru da su ba.
Sai wajen karfe tara sannan Hajia ta shirya suka kama hanya tare da Habib din da Mustapha suka koma gidan.
PAGE 229
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
A cikin tashin hankali suka sami yaran, Nasreen da Shukra suna sanye da uniform dinsu; don saida suka fara shirin makaranta sannan Naja ta sauko ta sanar da su ba zasu makaranta ba Habib ya bata Abbansu kuma ya tafi nemansa.
Babu wanda ya ji shigowarsu gidan saboda Mustapha a waje ya ajiye motarsa saboda Hajia tace yanzu zata fito ya mayar da ita. Da sallama suka shiga parlor di, Nasreen ce da Shukra suna zaune a parlor din da flask din shayi a gabansu da katon bread. Sai dai sun kasa shan sahyin sun yi tsuru-tsuru.
Da gudu suka mike, Shukra ta fada jikin Habib tana dariya yayinda Nasreen ta matsa kusa da Hajia. Suka karasa ciki suka zauna.
Hajia tace ‘Ina Afaf?’
Nasreen tace ‘Tana dakinmu.’
‘Antin fa da Rukayya?’
Nasreen ce ta sake sunkuyar da kai tace ‘Basu sauko ba.’
Hajia tace ‘To kije ki kirawo min ita kice ta zo.’
Shukra tace ‘Yanzu fa ta leko kuma tace kada wanda ya hau mata sama ya dameta, ko menene a jira sai ta sauko.’
Hajia ta jijjiga kai, ta kalli Mustapha.
Ya dan diririce sannan yace ‘Hajia tasowa zakiyi muje saman ai.’
Ba tare da wani musu ba ta mike ta tasa Nasreen da Shukra a gaba tana biye da su yayinda Mustapha da Habib suke biye da ita.
Anti Wiyya ce a zaune a kan kafet da kwanuka a gabanta suna cin abinci ita da Rukayya yayinda Naja take zaune a kan kujera tana cin nata abincin suna hira. Da yake kicin a buda yake ana hango mai aikinta da goyon baby tana goge-goge.
Shukra ce ta fara shiga tana surutu don haka a fusace Anti Wiyya tace ‘To sarkin tsurku, ba cewa aka yi ku zauna a kasan ba shine kika shigo kina….’
A lokaci guda kuma Naja tace ‘Ai sai nayi maganin wannan yar…’
Sallamar Hajia ce ta katse musu zantukan, ta karsa ciki yayinda Shukra ta zagaye ta koma bayan Abbanta. Suka karasa ciki suka zauna yayinda Naja da Wiyya suka diririce.
Naja tayi wuf ta mike ta kwashi kwanukanta tana cewa ‘Bari na wanko hannu.’ Ta nufi kicin cikin sauri.
Itama Wiyya ta kwashi nata kwanukan ta mike tana cewa ‘Sannu da zuwa Hajia, bari na kawo miki abinci.’
PAGE 230
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Rukayya tace ‘Anti ban koshi da naman ba.’ Bata ko saurareta ba ta wuce kichin yayinda ita kuma ta tashi ta bi bayanta da sauri.
Sai dai duk saurinsu kowa ya riga ya ga abinda yake cikin kwanukan nasu; farfesun kaji ne wanda suke hadawa da burodi da shayi suna ci.
Bayan sun zauna Hajia ta dubi Mustapha sannan ta dubi Nasreen tace ‘Nas ku ina naku naman naga kuna cin gayan burodin.’
Tayi darya tace ‘Ba a bamu ba, dama kullum abincin sama da ban da na kasa har garama idan Abban yana nan.’
Hajia ta sake kalloshi tace ‘Allah ya sauwake.’
Naja ce ta dawo parlor din ta zauna a kan kafet ta gaida Hajia, bayan ta amsa ta dubi Nasreen tace