ja dogon tsaki ya mike a fusace ya fice daga dakin.
PAGE 206
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta zuba fuskarta a tafukan hannayenta, so take hawayenta ya fita ko zata samu taji sanyi a ranta amma hawayen ya bushe kyamas. Kirjinta har zafi yake saboda yanda zuciyarta take turiri; Mommy ce ta fara yi mata wannan zargin gashi yanzu Mustaphan ma da shi da ‘yanuwansa suna zargin ta zubar da cikin ne don yaje da ita Hajji. Tabbas Allah sai ya bi mata hakkinta.
Haka ta kwanta zuciyarta na mata zafi saboda takaici; ta so ta kirawo Mommy ta gaya mata ko zata sami salama a ranta, to amma hakan ba zai yi mata wani amfani ba. Tunda Mommy din ce ta fara yi mata wannan zargin. Ta sake fashewa da kukan takaici ta gyara kwanciyarta; yau itace da kwana amma ta san yanda Mustapha ya fice daga dakin nan watakila sai dai idan ya dawo daga aikin hajji sannan ya waiwayeta.
………
Ranar laraba aka kirawo su Mustapha, jirginsu zai tashi karfe biyar na yamma don haka aka basu shawara su kasance a cikin airport din tun kafin azahar. Sun gama hada kayansu shi da Najan kuma ya riga ya sanar da Khadeeja, ya danka mata duk wani abu da take bukata don kula da gidan.
Wajen karfe sha daya yana zaune a parlor dinsa shi da yara Khadeeja ta fito daga dakinta ta shige kitcen don dora abincin rana. Ya tsallake yaran ya bi bayanta ya tsaya daga kofar kitchen din ya rungume hannuwansa a kirji sannan yace ‘Kada fa ki dafa abincin da ni yanzu zamu wuce airport, ki dafa ke da yara kawai.’
‘To.’ Ta amsa murya kasa-kasa.
Ya kula tunda sukayi maganar zubewar cikinta take son tada masa fitna shi kuma ba zai saurareta ba, fata yake kawai Naja ta gama hada kayanta su fice su bar mata gidan kafin ta takalo rigima. Don haka ya juya ya koma cikin yara ya zauna.
PAGE 207
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Har ta dauko tukunya zata dora shinkafa sai kuma ta fasa, ta ajiye tukunyar ta fito daga kitchen din ta koma dakinta. Tana shiga ta wuce gaban mudubi ta ja kujerar ta zauna; bata san me ya sa ta fasa dora girkin ta zo ta zauna ba. Kamar dai tana bukara wani wanda zasu yi magana ne amma ta rasa wanda zata gayawa damuwarta ya fahimceta. Ta daga fuskarta ta kalli kanta a cikin mudubin, at yiwa kanta murmushi sannan ta sake sunkuyar da idanuwanta. Yanzu haka zata cigaba da rayuwa a gidan nan a matsayin ‘yar aiki? Tunda matsayinta bai wuce hakan ba, duk wasu alamu sun nuna. Mustapha ya tabbatar mata ba zai taba iya yi mata adalci ba tun ma tana ita kadai matarsa balle yanzu da ya hadata da wadda yake kauna. Ta sake daga ido ta kalli kanta a mudubin; to wai zaman me take a gidan Mustapha ne? Shi dai ya gama nuna mata ba zai taba canzawa ba; duk wani abu da yake yi mata a halin yanzu zata iya yiwa kanta. Bukatar aure ce kawai wadda dama sai ya gama dama yake zuwa wajenta tunda ta daina binshi dakinsa. Ta yanke kauna daga samun adalci a wajen Mustapha komai yawan kaunar da zata nuna masa da kulawarta ga ‘yayansa. Ta tabbatar shi ba zai iya nuna mata kauna da kulawa ba; watakila sai dai idan ana kwatan soyayya ta kwata ta karfin tsiya daga wajen Mustapha; to idan sai an kwata kuma ya koma ba so ba. Ta ja gwauron numfashi, ta zuba fuskarta a tafukan hannayenta, dumin hawayenta ne ya sa ta daga fuskar tata ta kalli hawayen da ya diga a hannuwanta. Ta jijjiga kai tana murmushi a lokacin da hawaye yake gangarewa a kumatunta; ta gaji, ba zata iya ba, ta gaji da wannan kokawar, ta gaji da kokawar kwatowa kanta mutunci da so a wajen Mustapha, ta gaji ba zata iya cigaba ba.
Ta mike kamar wadda aka tsikara ta nufi gaban wardrobe, ta sauke akwati ta fara zuba kayanta. Ba zata iya cigaba da wannan rayuwar ba, gara kawai ayi ta ta kare.
A hankali ya turo kofar dakin ya shigo da sallama, fuskarta fayau kamar ma farinciki take. Ta dubeshi ta amsa sallamarsa ta cigaba da jera kayanta a cikin akwatin. Ya dubeta da mamaki yace ‘Ya naga kina hada kaya, ko wardrobe din kike gyarawa?’
PAGE 208
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta dan tsaya da zuba kayan ta kalleshi tace ‘No ba gyarawa zan yi ba, gidan mu zan tafi.’
Mamakinsa ya karu, ya karsa matsawa kusa da ita ‘Ban gane gidanku zaki tafi ba bayan yanzu zamu tafi, shigowa ma nayi na gaya miki ki fito kuyi sallam da Naja zamu wuce.’
Ta rufe akwatin ta zuge sannan ta juya cikin wardrobe din ta dauko jakarta ta sake ajiyewa a kan gadon. Ta kalleshi tace ‘Ka bani minti biyar na karasa hada kayana na fita sai ka rufe gidan gaba daya don nima gidanmu zan tafi.’
Ya dan fara fusata ya matsa ya sha gabanta yana cewa ‘Bana son wulakanci Khadeeja, wai ke me yasa ne duk lokacin da mutum yake cikin uzuri yake so kiyi masa wani abu sai kin yi fitna ne? an gama magana dake amma yanzu saboda kina so ki sa muyi missing flight zaki fara maganar zaki tafi gida.’
Tayi murmushi ta daga kai ta kalleshi tana cewa ‘In sha Allahu wannan itace fitna ta karshe da zan yi maka Mustapha,