shekara nawa zan yi da Mustapha ba zai taba canzawa ba, ba zai iya yi min adalci ba. Watakila ya daina so na, watakila kuma iya son da yake min kenan. Amma dai gaskiya na gaji Mommy.’
Ta dafa hannunta cike da kulawa tace ‘To ai hakuri zaki yi, dama shi aure ya gaji haka kuma ribar aure ta me hakuri ce. Baki sani ba ko ita abokiyar zaman naki wani abun take yi na biye-biyen malamai, ai duka ana yi.’
Tayi murmushin yake tace ‘Ai wallahi babu wani biye-biye Mommy, a hayyacinsa yake yi. Kawai dai idan hidima za ayi masa to ya fi so ni ya saka ni aiki, idan kuma morewa zai yi da harkar soyayya to wannan ita ta iya. Amma babu wani asiri haka ya tsarawa kansa.’
Ta sake kama hannunta tarike tana kallon fuskarta tace ‘Ki dai yi hakurin, in sha Allahu zaki ga ribarsa. Kuma idan dai Hajji ne da izinin Allah kema zai kirawoki.’
‘Uhm.’
Nan suka dauki lokaci Mommy tana bata baki. Can zuwa yamma ta shirya Ahmad ya mayar da ita gida ta barwa Mommy Hammad.
--------
Shirye-shiryen tafiya aikin Hajji sun kankama domin ana maganar saura sati uku alhazai su fara tashi. Duk wani abu da suke bukata na kula da gida Mustapha ya tanada ya kawo musu, kuma yayi mata bayanin abokinsa wanda dama ta san shi; shine zai kawo musu raguna kuma ya tsaya a yanka.
Yanzu kullum sai yamma tayi sai ya dauki Najan a mota su fice wai sun tafi bita, haka ta zuba musu ido tana ta bawa kanta hakuri.
PAGE 202
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Gaba daya maganar tafiyar ta fita daga ran Khadeeja, kuma Mustaphan ma gaba daya ya fice mata daga rai; ji take yi kamar matsayinta a wajensa bai wuce na mai aiki ba. Zuwa yanzu ta san wanda ma bai san halin da suke ciki ba ya san Naja tana da ciki domin tara yawunta ya karu kuma tayi fari tas irin na masu ciki. Sai dai har yanzu ita Khadeejan bata sanar da Mustapha cewa ta san Najan tana da ciki ba. Sai shirye-shiryensa yake yi yana zuwa sallama da mutane domin Hajia ta gama gayawa kaf dangi Mustapha zai tafi Hajji da matarsa. Danginsa da na Naja sai zuwa suke sallama, duk wanda ya zo sai ya cewa Khadeeja Alah ya kirawo ‘yan baya. Wannan kalmar ba karamin bata mata rai take yi ba, amma haka ta share ta kawar da kai.
Tun jiya bata jin dadi sai dai bata gane me yake damunta ba, haka take ta fama. Da yake ba itace da aiki ba kuma Hammad baya nan haka ta wuni a kwance. Daf da magriba ta fara gane abinda yake damunta; marata ce take ciwo ga wani amai da yake taso mata amma ya ki fitowa. Haka ta sha panadol ta shige dakinta ta kwanta. Wajen 9pm Mustaphan ya shigo dakin domin sanar da ita ya dawo kamar yanda ya saba. Har ya juya zai fita ya dan tsaya yace ‘Wai ya na ganki a kwance ne? kamar baki da lafiya.’
‘Uhm, mara tace take dan ciwo.’ Ta amsa a gajiye.
‘Ok, Allah ya sauwake. Ko kina bukatar wani abu?’
Tace ‘No ina jin zai daina don na ma sha panadol.’
Ya sake yi mata sannu sannan ya juya ya fice.
Can wajen 10:30pm ciwon ya matsa mata, tun tana daurewa har ta kasa. Ta lalubi wayarta ta kirawoshi, ba tare da bata lokaci ba ya shigo dakin nata. Kafin ya shigo ma ta riga ta shige bandaki saboda yanda take jin kamar zata yi kashi, kafin ta karasa toilet din abinda yake shirin fitowa daga jikinta ya riga ya fito sai jini da ya biyo baya gaba daya da aman da ya tokare mata kirji.
A tsugune ya sameta a bandakin, ya karasa da sauri ya duba halin da take ciki. Ya kamata ta mike sannan ta karasa ta zauna a kan toilet. Tace ya jirata ta wanke jikinta sai suje asibiti.
PAGE 203
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Nan da nan ta wanke jiki ta gyara sannan ta tattare zanin nata da bainda ya fita daga cikin nata gaba daya ta saka a leda sannan ta fito ta shirya suka kama hanyar asibiti. Babu wanda yayi magana sai shi da yake mata sannu lokaci zuwa lokaci; a haka har suka isa asibitin.
Ba tare da bata lokaci ba likita ya dubata kuma ya tabbatar da cewa cikin jikinta ya fice gaba daya, don ko wankin ciki ma ba sai an yi mata saboda komai ya fice. Aka rubuta mata magunguna aka sallamesu.
Tun a mota ta gane Mustapha bai ji dadin zubewar cikin ba, duk da ita ta fi shishiga damuwa da zubewar cikin; amma dai ta kula ba haka yayi ba wancan lokacin da tayi bari. Har yanzu tana jin ciwon mara don haka ba zata iya surutu ba.
Bayan sun dawo gida ta haye samanta ta sake yin wanka sannan ta sha magungunanta ta saka Hafsa ta hada mata indomie da shayi mai kauri ta zauna taci. Sai da taci ta koshi sannan ta kirawo Mommy da Yaya Mama ta sanar da su. A daren Momy ta so zuwa sai da Khadeejan ta hanata ta sanar da ita cewa ta sami lafiya su bari da safe sa zo; don haka suka hakura.
Can wajen daya saura ya sameta a dakin; tana kwance a gefen gado tana shirin yin bacci. Ya zauna a gefenta yace ‘Sannu.’
‘Yauwa.’ Ta amsa tana daga kwance.
Suka yi shiru na dan lokaci, ta san da zance a bakinsa don haka tayi kasake tana jiran taji me zai ce. Jimawa kadan ya gyara zama kamar wani mara gaski