NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 77 of 105

ga gefe a kan kafet; yanayi zaman da Mustaphan yayi kawai ta kalla ta sha jinin jikinta. Ko da bai kai kararta gida ba to tabbas ta san a wannan dan zaman da Baffan yayi ya gaya masa laifinta. Ta karasa ta ajiye ruwan a gaban Baffa a daidai lokacin da Naja wadda itama ta shigo ta gaisheshi take ficewa daga parlor din. Ta zauna daga gefen kafarsa sannan ta gaisheshi ya amsa cike da girmamawa. Sai da ya gama raha da yaran sannan ya zaro sababbin kudi a aljihunsa ya bawa kowa naira dubu sannan ya sallamesu suka wuce suka barsu daga shi sai Khadeejan da Mustapha. PAGE 182 MIJIN MARIGAYIYA A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal) Ya dubi Khadeeja yayi gyaran murya sannan yace ‘Deeje, garin yaya kika ce ba zaki taimaka ki karbarwa abokiyar zamanki hidimar gida ba bayan bata da lafiya? Haba Khadeeja, hakan ai shine zaman tare tunda dai Allah ya hadaku.’ Ta yi shiru ta sunkuyar da kai tana tunanin ta inda zata fara, inama da Baffa ya zo da Mommy. To ta ina zata fara gayawa Baffa yanda Mustapha yayi mata lokacin tana nata laulayin? Kuma ya za ayi ta gayawa Baffa cewa ita bata bin Mustapha dakinsa kuma duk ranar da bata bishi dakinsa ba Naje yake kira ta tayashi kwana? To ai Baffa ma sai dai ya sake yi mata fadan kin zuwa dakin miji domin tabbas abu ne da haka aka saba; kuma ta sani mata biyu ne da kakanta mahaifin baffa. Wanda da wayonta kafin dukansu su rasa ta san matan ne suke zuwa dakinsa. Wannan kam ai sai dai ta kara kai karar kanta. Muryar Baffa ce ta katseta yana cewa ‘Deeje me yasa ba zaki taimakawa abokiyar zamanki ba?’ Ta dan yi firgigit kamar wadda aka tasa daga bacci sannan tace ‘Uhm Baffa wallahi nima daurewa nake ina yin hidimar ranar girkina, tunda ga jego ina yi sannan kuma ina zuwa aiki.’ ‘Eh, ai wannan ba zai gagareki ba tunda kinga da ace ke kadai ce a gidan ai duka zaki hada ko?’ Suka yi shiru na dan lokaci sannan daga baya tace ‘Baffa nima fa haka nake hada nawa laulayin da aikin gidan babu wwanda yake tayani. Kuma ka ga Baffa akwai mai aiki fa wadda zata iya yi mata duk abinda take so idan tayi mata bayani.’ Baffa ya dan yi murmushi sannan yace ‘Na fahimceki Khadeeja, amma dai kiyi hakuri ki karbar mata aikin. Tunda kin ga yanzu kema idan kika kuma samun wani cikin ai zata karbar miki ko? Kiyi hakuri Deeje, bana son taurin kai da yawa. Allah zai baki lada har kashi biyu, ladan biyayya wa miji da kuma ladan taimakon ‘yar uwarki musulma wadda take neman taimakon naki. Kiyi hakuri kin ji, tunda ga yarinyarki nan tana taimaka miki ki zauna lafiya tunda dama yara duka naki ne tun kafin ma a aurota.’ Haka Baffa ya dauki lokaci yana bata hakuri, daga karshe kuma ya bata umarnin lallai ta taimakawa Naja ta karbi hidimar gidan. PAGE 183 MIJIN MARIGAYIYA A Hausa Novel by Sakina Yazid Innar su Amal Bayan ya mike duka suka mike gaba daya, a nan yayi sallama da Khadeeja yace ta koma ciki. Suka fice shi da Mustapha wanda yayi masa rakiya har wajen motarsa sannan yayi masa sallama ya tafi. Ya san ko da ya koma wajenta a yanzu ba zata saurareshi ba sai dai ma ta gaya masa maganganun da baya son ji, don haka ya wuce wajen Naja tunda dama kwananta ne. ………. Har turiri take ji yana taso mata a kirjinta saboda tsabar yanda zuciyarta take tafasa; sai da tayi da gaske sannan ta kai kanta dakinta ba tare da tarushe da kuka ba. Ya za ayi ace ta karbarwa naja girki saboda kawai tana da ciki? Bayan ita a lokacin da tana da nata cikin hakaya dinga barinta da duk wata hidima yana hana yaranshi su tayata. Sannan kuma idan tayi magana ya dinga nuna mata cewa laulayi ba komai bane kamar ma dai itace take son nuna raki. Yanzu kenan haka zata kwashe wata takwas ko tara tana kula da yara yayinda Naja take kwana da miji tunda laulayin bai hana idan ta sameshi shi kadai a dakin ta kai masa kanta ba? Tana shiga ta murza mukulli ta rufe kofar, sai da karasa kan daddumar da ta tashi sannan ta zube da gwiwoyinta tarushe da kuka. Shikenan ita ta zama baiwar Mustapha ne? ya iya nunawa kowa kauna da tausayi a duniya amma banda ita? Anya zata iya wannan rayuwar a gidan Mustapha kuwa? Amma ta san dole ne ta bi umarnin Baffanta, musamman da yake a gaban Mustapha ya bata umarnin. Ta kifa goshinta a kasa ta sake rushewa da kuka. ….. Ya so kwarai kamar yanda ya saba lekawa da daddare ya yiwa wadda bata da kwana sai da safe ya leka wajen Khadeeja, amma da yake bai shirya rigimarta ba sai kawai ya kyaleta suka shige daki shi da Naja suka yi kwanciyarsu. Ba karamin dadi ya ji ba da ya dawo daga masallaci sallar asuba ya jiyo motsinta a kitchen, tabbas ya san ta ji maganar Baffanta. Ba tare da bata lokaci ba ta shiryasu sannan ya fito ya kaisu makarantar. Kafin ya dawo daga kaisu makaranta ta gama nata shirin, a zaune ya sameta a parlor dinta tana karyawa. Babu yabo babu fallasa suka gaisa, sai dai daga gaisuwar bata sake ko da kallon inda yake ba. PAGE 184 MIJIN MARIGAYIYA A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal) Jimawa kadan ya mike zai
🏠