da ai a nan zamu kwana.’
‘Oh,..’ sai kuma ta dan sunkuyar da kai kamar dai ta kasa fadin abinda take son fada ne. ya kurbi shayi ya bita da kallo yana jira ta karasa fadin abinda ta fara fada.
‘Gaskiya mu kwana a dakina, in ya so duk ranar kwana kai sai ka dinga zuwa dakina muna kwana.’
Da mamaki yake kallonta yana dariyar yake ‘Khadeeja a ina kika taba jin miji ya bi matarsa dakinta kawai saboda su biyu ne? shike nan yanzu duk wacce take da kwana nine zan je dakinta kenan?’
Ta dan bata rai ‘Nifa ba haka nace ba, ita idan tana so ta dinga zuwa dakinka bani da matsala da hakan amma ni dai sai ka dinga zuwa dakina.’
PAGE 172
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Dariya ma maganar tata taso ta bashi; tunda yake bai taba jin inda maigida yake bin dakin matansa ba sai dai a inda bashi da dakin saboda kankantar gidan ko kuma agidan haya. Amma ya za ayi yana da gida kamar wannan ga dakinsa da parlor dinsa amma ace shine zai dinga bin mace dakinta? Allah ma dai yasa Khadeeja wasa kawai takeyi.
‘Tunda kike don Allah kin taba jin inda aka ce maigida kamar wannan yana bin matansa daki saboda kwana madadin su suje dakinsa?’ Ya tambayeta yana nuna gidan, sannan ya cigaba ‘Kuma ma a wanne karatun aka biya miki haka bayan ga yanda kika taso kika ga ana yi?’
Ta kalleshi ta marairaice da fuska tana cewa ‘Don Allah ka bari mana, na ga dakin nawa ma duk gidanka ne ai meye don ka kwana a ciki. Itama Najan idan tana bukatar hakan ba sai kaje dakinta ka kwana ba?’
‘Oh, nine ma zan dinga binku ina kai muku kwanan kenan?’
‘To meye a ciki, abu ne fa wanda ya zo a tarihi ma.’
Ya dan zaro ido yana kallonta ‘Wanne tarihin Khadeeja? In ce ko dai tarihin tsumburbura ne?’
Ta kula dai so yake ya raina mata hankali, kuma idan bata yi da gaske ba so yake ta dinga zuwa dakinsa kwana. ita kuma gaskiya bata jin zata iya kwanciya gadon da ya kwanta da wata matar ko da kuwa ba Naja din bace. Gara kawai ya dinga zuwa dakinta. Ta kara bata fuska tace ‘To a islamiyya dai tunda ake buya mana sirah sai dai ace Annabi SAW ya je dakin Aisha, ko yaje dakin Hafsa da sauransu, duk bayanan da aka yi mana sun nuna shi yake zuwa dakin kowacce. Kuma tunda dai auren nan shi ake kwaikwayo SAW ai ba zai zama matsala ba idan an kwaikwayi wannan din ma.’
Bude baki yayi kawai yana kallonta; ya rasa yanda aka yi Khadeeja take lale shi haka har take samun damar gaya masa duk maganar da ta ga dama. Ya jijjiga kai yace ‘To idan nace ba zan zo ba fa sai dai ke ki zo dakin nawa?’
Tayi murmushinta wanda yake kara bashi mamaki; kana cikin magana da ita fuska murtuke sai kuma ta koma murmushi har kaga kamar da zuciyarta take murmushin, haka ma kuma idan tana walwala lokaci guda zata sha kunu ka zata kamar bata taba murmushi ba.
PAGE 173
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Muryarta ce ta katse masa tunanin tana cewa ‘Na san ma ba zaka ce hakan ba, kai da gidanka. Abinda ko a parlor ka kwana babu wanda zai nuna maka yatsa balle don ka kwana a dakin matarka?’
Binta kawai yake da kallo yana jijjiga kai, yace ‘Toh tsarani Khadeeja.’
Tayi dariya tana mikewa tsaye tana cewa ‘To ina laifi, yaushe rabon da a tsaraka.’
Kasa magana yayi kawai ya dinga binta da kallo har ta gama kwashe kwanukan. Bukatar ta yakeyi saboda shi kansa ya san yayi kewarta, don haka ma baya son yaja rigima a wannan daren da yake son ya huce gajiyarsa. Gashi sai kaiwa da kawowa takeyi tana kwashe kwanuka tana juya jikinta kamar da gayya, ya ma rasa me zai ce mata.
Bayan ta gama kwashe kwanukan ta dafa kafadarsa tace ‘Sai ka shigo.’
Bata ko saurari amsarshi ba wuce dakinta ta barshi a nan.
Sai yau ya tabbatar Khadeeja ta raina shi; tunda yake bai taba ganin matar da idan tayi niyyar abu sai tayi shi ba ko da tsiya ko da tsiya-tsiya sai Khadeeja. Anya kuwa ba wani abu Khadeeja tayi masa ba; idan taga dama ta gwada masa taurin kai da fitan idan kuma taga dama ta mayar da shi kamar wabi sakarai tayi masa wayo? Amma dai gaskiya ba zai juri binta dakinta ba dole ta hakura tayi yanda aka saba wato duk mai kwana ta bi miji dakinsa.
Babu yanda ya iya da yake shine yake da bukatarta dole ya tashi ya bita dakinta; kafin yaje ma bacci ya riga ya kwasheta. Don haka sai da ya tasheta ta sake lallabata sannan ya sami biyan bukatarsa.
………..
Washegari ya kama ranar asabar ce don haka yara basu da makaranta; ko da ya dawo daga masallaci a kan dadduma ya sami Khadeeja a dakinta tana azkar, bayan ta idar ta gaisheshi sannan tace ‘Mantawa fa nayi jiya ban gaya maka yau ne bikin su Fatin Baba Sani wanda na nuna maka invitation din last week.’
Ya gyara pillow ya kashingide a kan gadon yana cewa ‘Ok, Allah ya sanya alkhairi. Ai in sha Allahu nima zani daurin aure don Baffa da kansa ya turo min kati.’
‘Ok. Ni sai wajen azahar zan tafi don ka ga ban je yawon arba’in ba sai na hada gaba daya, idan na kwana biyu a gidan Mommy