kuma suzo suna celabrating a gaba na?’
Da mamaki Mommy tace ‘Ikon Allah, ita mahaifiyar tasa ce zata yi biki saboda zai kara aure?’
Ta sa hannu ta goge ragowar hawayen da yake kan fuskarta sannan tace ‘Eh Mommy, wai zasu zo suyi biki. Kin ga kenan nace ba zan karbi amarya ba amma zasu yi min dole.’
Mommy ta kama hannunta ta kalleta sannan tace ‘Kiyi hakuri kin ji, zaki iya. Kishiya bata kashe kowa ba in sha Allahu kema ba zata kashe ki ba. Ki bi su a hankali, dare daya ne ayi ya wuce. Da an kwana biyu itama zata zama kamar ke kuma yanda yayi miki haka zai yi mata.
Ta jijjiga kai tana murmushi mai dauke da ma’anoni tana cewa ‘Hmm! Mommy ba zai taba yi mana adalci ba. Kina ganin yanda tum kafin ta shigo shi da yaransa da ‘yanuwansa suka karkata wajenta. Gaskiya ban saka rai Mustapha zai iya yi min adalci ni da matarsa, sai dai kawai nace Allah ya bani hakuri ko kuma ya kawo min mafita mafi alkhairi.’
‘kada ki damu, ai ba shi yayi kansa ba, in sha Allahu Allah ba zai bari ya cutar dake ba daga shi har ‘yanuwan nasa gaba daya.’
‘Hmmm!’ ta sunkuyar da kai tana kallon yatsinta da take wasa da su.
Jimawa kadan tace ‘Mommy bana son ayi min biki a gida, bana son a akwo min maryarsa ace za a bani amanarta ko ayi mana fada tare. Amma kinga duk sun shirya hakan zasu yi.’
PAGE 138
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Mommy ta sake kamo hannuwanta duka biyun ta kalleta suka hada ido sannan tace ‘Kada ki damu, kamar yanda na gaya miki na ranar ne kawai. Kuma kema ‘yan uwanki zasu zo, duk da kince kada azo da yawa toh yayayrki zasu zo da kamar mutum hudu haka. Nabila kuma tace gobe zata taho ta tayaki kwana zuwa lokacin da zasu gama bikin. Kada ki damu in sha Allahu omai zai wuce.’
Haka suka zauna Mommy tayi ta bata baki har zuwa yamma. Ta samu zuciyarta tayi sanyi amma dai bata da tabbacin ko zata iya dauka, ta dai hakura taga yanda zata kaya kamar yanda Mommy tace.
Sai da yamma sanna ta shirya ta koma gidan zuciyarta cike da wasi-wasi.
Washegari ‘yan uwan amarya suka zo suka yi kafi. Basu ja fitna ba don haka lafiya aka rabu, ta sa Hafsa ta mika musu kuloloin abincin da ta bayar aka dafa musu; don ita tunda suka shigo gidan ta haye sama kuma har suka gama bata sauko sun hadu ba. Sun tura Hafsa taje ta kirawota sau ba iyaka amma haka hafsan take dawowa tace musu saman a rufe yake. Haka suka gama kafinsu suna ta rangada guda, ga turare da suka bade gidan dashi. Sai da suka kusan gamaw sannan yara suka dawo daga makaranta, nan da nan suka shige cikinsu da yake sun saba da kannenta saboda yawan zuwa gidansu da suke yi.
……….
Dawowarsu daga gidan kafi yayi daidai da dawowarta daga wajen lalle, a zaune ta samesu a farfajiyar gidan ana ta hirarraki. Ta dubi yayarta Ummi tace ‘Yaya har kun dawo daga kafin?’
Ta tabe baki tace ‘Hmmm! Mun dawo’
Ta dan kalleta da alamar tambaya tace ‘Ya naga kina yatsina fuska? Komai dai ya tafi dai-dai ko?’
Salma wadda cousin dinta ce tace ‘Um babu laifi. Amma fa mu a kasa Mustaphan ya nuna mana daki guda daya da parlor yace nan ne naki kuma a nan mukayi kafi. Saman gidan nan ma dai ‘yar mulkin uwargidan taki bata ko bari mun hau ba ta ja kofa ta rufe don bamu ko isa ta sauko mu gaisa ba ta aiko mana da kulolin abinci kamar wasu mayunwata.’
Ta zmburi baki ‘Ban gane a kasa ya baku daki ba? Ai ni sama mukayi da shi kuma ya amsa min a kan haka.’
‘To ai kuwa dai bai isa ba don Hajia Babba ta haye sama, bata ko saukowa idan bata bawa bako mahimmanci ba.
PAGE 139
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Nan da nan idonta ya kawo kwalla, ta mike ta daga waya ta nufi cikin gidan. Ba tare da bata lokaci ba Yaya Ummi ta mike ta bi bayanta. A daki ta sameta har ta lalubo lambar Mustapha zata buga. Ta dafe wayar tace ‘Ba sai kin kirawoshi ba domin karya kawai zai yi miki ya sake bata miki rai, alamu dai sun nuna itace mai gidan. Kada ma ki daga hankalinki a kan wannan maganar balle ki hanaku morar satin amarcinku, don in kika hana muku wannan kwankin to kin yi mata alfarmane don ita zata so haka. Ko da ma kunyi magana da shi din ki nuna masa babu komai.’
Ta kalleta tana zumbura baki tace ‘Yaya babu komai fa kika ce? Ai ba haka muka yi da shi ba. Tun lokacin da ya sayi gidan fa muka je dashi nace sama nake so kuma ya amince, shine zai je kuma ya canja magana.’
Tayi murmushi tace ‘Kika san me aka yi masa ya canza? Wannan mata duk da ban ganta ba amma na san a shirye take, idan bamu dage ba zuwa zaki yi ki zama ‘yar kallo don da alama tana shimfida mulki yanda ranta yake so.’
‘To yanzu ya za a yi?’
Tayi murmushi ‘Kada ki samu zan yi magana da Inna, dama kin ga tunda aka fara maganar bikin nan take faman nemar miki taimako. Kin ga yanzu sai a mayar da hankali ayi aikin da zaki hada kan gidan ki mallake a sauke miki ita daga benen kuma a cireta daga zuciyarsa gaba daya.’
‘Anti dama fa bata zuciyarsa