Allah can. Gaskiya kia gaya musu mune a sama.’
‘Hmm! Zan fada musu Shukra, ai mune a sama kada ki damu.’
Ta cigaba da surututa tana bawa Khadeeja labarin irin abubuwan da suke yi idan suka je gidan Naja.
PAGE 128
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Duk da Khadeeja bata yi mamakin jin cewa Naja ta san da sabon gida ba amma ta yi mamaki da ta ji cewa har Naja ta zabi part din da take so yainda ita kuma har yanzu bai ma gaya mata ita da wata matar zasu zauna a gidan ba. Ta kasa gane dabarar da Mustapha yake jin yayi da yaki gaya mata zai yi aure; amma dai zata cigaba da binsa taga karshen wulakancinsa. Ko da yake a ‘yan kwanakin nan ma yanda yake kara tubure mata ta tabbatar da tana biye masa da kullum sai sun yi fada. To sai dai bata da wannan lokacin tunda ga project dinta wanda take so ta gama kafin su fara jarrabawa wanda tana fatan Allah ya sa kada haihuwa ta zo mata har sai tayi final paper.
Haka ta ajiye wannan ma a ranta tana jiran ranar da zata titsiye Mustapha tunda haka ya zaba.
……..
Tun kafin su fara jarabawa ya sanar da ita idan ta haihu aka yi suna aka gama zuwa barka zasu koma sabon gida, saboda baya so aje a bata masa gida. Itama tsarin yayi mata don haka ba tare da wata matsala ba ta amsa. Kuma kamar yanda ya bata umarni ta fara hada kayanta da zata tafi da su duk da cewa ya gaya mata ya saka sabbin furniture a gidan.
Ranar da zata yi jarrabawar karshe ya kama yara suna hutun makaranta, kuma sai 2pm zasu shiga paper. Don haka yace idan babu matsala yanaso ta shirya da wuri su tsaya a sabon gida taga furniture din da ya siyo in ya so sai ya ajiyeta a makaranta shi da yara su wuce wajen Hajia. Ta riga ta gama karatunta don haka tun wajen sha daya ta shirya suka shiga mota gaba dayansu suka kama hanya.
Saman gidan yana dauke da parlor guda biyu karami da babba da kuma dakuna guda uku sannan da kitchen, daki daya da parlor suna tare da juna wanda dama ya sanar da ita nan ne nashi part din. Kasan kuma parlor ne guda daya, sai dakuna guda biyu wadanda suke kusa da juna sai kuma wani dakin guda daya wanda yake gafe, sannan kuma da kitchen. Parlor din kasan duk a nan aka sauke furniture din; duk da kusan kowanne yana cikin kwalinsa.
Suna shiga suka dan yayyage kwalin ita da yara suka gani.
PAGE 129
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya dubeta yana nuna dakunan kasan yana cewa ‘Sai ki zabi a wane dakin za a saka miki gadon, in ya so daya dakin kuma sai a dauko gadonki na tsohon gida a saka.’
Ta kama hanyar sama tana cewa ‘Eh hakan ma yayi; dakin wanda yake jikin nakan sai saka min sabon gadon a nan in ya so na kusa da shi sai a gyarwa ‘yan mata na ko? Shi kuma Yaya Habib sai a bashi wannan na kasan.’
Shukrace kawai ta biyota shi yana tsaye a inda yake. Ta dan juyo tana cewa ‘To kazo muje mana ka gani.’
Yayi ‘yar dariya yace ‘Na zata zaki fi son wadannan dakunan na kasa ai, kin ga sun fi girma. Kuma ai ina ga zai fi min privacy ace dakinki yana nan kasa a madadin yana kusa da nawa idan kin yi baki ina jiyoku.’
Tayi dariya tace ‘Haba dai, kuma don nice duk fadin gidan nan sai na rasa wajen sauke baki sai bedroom? Ai dama sama ba wajen saukan baki bane tunda nan kasan ma da parlor. Amma dai can ne dakina, in ya so idan ma baka so yaran su hau sama za a iya barinsu a kasa.’
Shukra tace ‘Gaskiya Abba mune a sama mu da Anti, in ya so ita Anti N…’
Kafin ta karasa Afaf ta katseta cikin daga murya tana cewa ‘To baki ji me Abban yace ba, kasan ya fi girma ne da space.’
Khadeeja tace ‘To mu dai ba ma son kasa, muna sama abin mu.’
Ta ja hannun Shukra suka haye saman.
Habib wanda yake tsaye a kusa da Abban nasu ya dubeshi yace ‘Haba Abba, dama ai sama na Anti Khadija ne.’ Kallon da Abban yayi masa ya sa ya kawar da idonsa da sauri ya waske yana cewa ‘Bari naje na tayasu zabn dakin.’
Haka ya hakura shima ya bisu saman inda khadeeja ta nuna masa dakin da yake jikin nasa tace shi take so, dayan kuma wanda yake gefe daya sai a barwa yara.
Bashi da wata hujja da zai bata a kan hanata daukan dakin sama, kuma har yanzu baya jin ya shirya gaya mata cewa zai kara aure, ya fi so sai ta haihu tukunna saboda kada ma yaji tausayinta idan tace zata tayar masa da hankali. Haka suka gama zagayensu a cikin gidan sannan suka shiga mota suka nufi BUK don su kaita.
PAGE 130
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Har suka isa makarantar bata daina mamakin Mustapha ba; ta kasa gane sai yaushe zai daina yi mata wannan karyar. Kuma ta kasa gane dalilin da yasa yake fifita bukatar Naja da son zuciyarta a kan tata, amma dai haka zata cigaba da biye masa ta ga gudun ruwansa.
………
Kwanansu biyu da gama jarrabawa Khadeeja ta haifi yaronta, don haka ko kwana bata yi a asibiti ba aka wuce da ita gidanta. Sai daga baya aka kawo mata Anti Binta wadda kanwa ce a wajen Mommy. Tun a asibiti Mustapha ya sanar da su ya sakawa yaro suna