NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 42 of 105

e ki cewa uncle ni bana son basket ball team ya barni na shiga football team. Haka kawai wai saboda ni dogo ne sai nayi basketball.’ Kafin Khadeeja tayi magana Najan tace ‘Au shine baka gaya min ba Habib, ai da ka gaya min nayi masa magana.’ ‘Dama Anti nake jira.’ Ya fada cikin halin ko in kula ya zari envelop guda daya daga hannun Najan ya mikawa Khadija yana dariya yace ‘Anti guess what?’ Ta dan yi murmushi yayinda suka bar Naja da baki bude, tace ‘What?’ Ya zaro takarda daya ya mika mata yana cewa 38 naci a Hausa yau don haka yau da shawarma zan yi dinner ko?’ Ta karba tana dariya sannan ta bashi hannu suka tafa tace ‘Iyye, ai dole kaci shawarma tunda yau ka wuce gori. Haba ko kai fa, kullum komai kaci A da B amma a Hasua ka dinga cin D da F.’ Ya mikawa Khaddeja envelop din yana cewa ‘To zaki ga Uncle din?’ PAGE 98 MIJIN MARIGAYIYA A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal) Tace ‘No, tunda yanzu ka ga kun riga kun fara games ina jin ka bari sai gobe sai na zo na ganshi. Kafin nan munyi tattauna a kan football da basketball din kuma mun yi magana da Abbanka ko?’ Ya gyada kai ‘Eh, hakane.’ Naja tayi sauri tace ‘Idan kina sauri ne ai sai naje naga Uncle din.’ Tace ‘No ba sauri nake ba, kamar dai goben zai fi dacewa kawai.’ Habib ya katsesu yana mikawa Khadeeja envelope din yana cewa ‘Anti sai mun dawo, goben kya zo kawai.’ Ya wuce ya barsu a nan. Naja ta mikawa Khadeeja hannu tana cewa ‘Ki kawo na tafiwa da yallabai takardun tunda office zan koma.’ Ta dan yi murmushi tace ‘No ina ga gara ni na tafi masa dasu tunda a gidansa zan kwana.’ Ta bata rai tace ‘Um, sai an jima.’ Ta wuce rike da takardun Afaf da suke hannunta Afafa din tana biye da ita suna hira. Khadeeja ta bi bayansu da kallo tana mamaki; to yaushe yayi sabuwar sakatariya? Tunda da dai ta san sakatarensa namiji ne. kuma har yaushe sakatariyar ta kai matsayin tazowa yara open day har tana wani cewa a bata takardu ta kai masa? Tukunna ma; kamar dai yaran nan sun sa wannan sakatariyar, itace bata santa ba. To kenan har yayi introducing dinta a wajen yaransa a matsayinta na wa? Me yasa suka kwana tare bai ce mata tazo open daya ba kuma bayan ya fita ma ya kasa kiranta? Wanda tunda ta aureshi duk wata harkar makarantar yara itace take zuwa kuma shi yake saka ta ta zo. To me yasa wannan ya sa sakatariya? Naja? Bata son ta yanke hukunci cewa akwai wani abu tsakanin Mustapha da Naja amma dai tabbas tana da tarin tambayin da zai amsa mata. Sai da ta raka Shukra aji sannan ta nufi fita daga makarantar. Tun kafin ta gama fitowa daga cikin ginin makarantar zuwa farfajiyar wajen da ake ajiye motoci ta hangosu, tana rike da hannun Afaf suna magana har suka karasa bakin motar gefen direba ta sa mukulli ta buda motar; ta dan ja baya ta labe. Me take gani ne? Motar Mustapha? To shine ya kawota ko me? Tana nan a labe ta hangosu; Naja ta bude motar ta zauna a kujerar direba sannan ta yiwa Afaf sallama ta ja motar. PAGE 99 MIJIN MARIGAYIYA A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal) Sai da ta karanta lambar motar a fili domin kara tabbatarwa motar Mustapha ce; kanta ya daure gaba daya. To me hakan yake nufi? Ya aiko sakatariyarsa ta zo wa yara open day kuma a motarsa. To hada kudi sukayi suka sayi motar a tare? Ko kuwa dai tsabar kauna ce ko rashin hankali ya sa suke sharing motarsa da sakatariya? Me yasa bai aikota a motar haya ba ko a motar office? Wato motar da ita idan dai makaranta zata ko arage mata hanya bata isa yayi ba itace ya bawa sakatariya take yawo a gari. Kai! Gaskiya Mustapha ya rainata. Tayi sauri ta fito daga inda ta rabe lokacin da ta hango Afaf ta nufo wajen. Tayi mata sallama sannan ta wuce ta fice daga harabar makarantar. A bakin titi ta tsaya, motocin haya sai tsayawa suke ba tare da ta hau ba; gaba daya ma ta manta inda zata saboda yanda zuciyarta take zafi; me Mustapha yake nufi da ita? Har ta juya zata koma gida saboda yanda take jin ba zata iya zuwa lecture din ba sai kuma ta tuna idan taje gidan me zata yi? Rufe kanta kawai zata yi a daki tayi kukan da ba zai mata maganin komai ba; don haka ta sake juyawa ta koma bakin titi ta hau motar BUK. Ta kalli waje ta tagar motar, tayi murmushi ita kadai; wai itace a motar haya yayinda ga wata can tana yawo a motar mijinta. Takawar da kai ta share kwalla. Ko da ta karasa makarantar ta san an riga an yi nisa da lecture din kuma ko ta shiga ma ta san babu abinda zata gane, don haka kai tsaye ta wuce hostel dakinsu Rahma inda suka saba zuwa su huta; duk da dai ta san suna wajen lecture amma ta san inda suke ajiye mukullansu. Tana shiga dakin tayi watsi da kayanta ta fada gadon Rahma ta kwanta ta fashe da kuka. Sai wajen karfe daya da kwata sanna suka shigo dakin suka sameta a kwance ta ci kuka ta koshi. Suna shiga Farida tace ‘Haba Malama, tun dazu muke kiranki a waya kin ki dagawa ashe kina nan abunki.’ Suka karasa suka fada kanta Asiya tace
🏠