ya suke so yayi? Ga lockdown an hana mutane fita sannan kuma su dauke masa mata. Kwana ukun nan ma da zai yi da yaran bai san ta ina zai fara ba don yana tuna yanda a kwana dayan nan suka gama firgitashi; ga gari a kulle balle ya kaisu gidan Umma. Gaskiya da an bude gari ranar asabar zai je ya dauko ta tunda dai ko shi ya tambayeta jiki ta ce da sauki.
Sai can da yamma dabara ta fado masa; ya dauki waya ya kirawo Baffan Khadija, bayan sun gaisa ya jajanta masa jikin Khadeejan sannan ya sanar da shi cewa ranar asabar idan aka bude gari zai zo ya dauki Khadeejan. Ba tare da matsala ba kuma Baffan ya amsa masa da hakan yayi, don haka cikin walwala ya karasa wuninsa. Bayan Ummi ta gama hada musu kayan shan ruwa shi da yara ta wuce ta tafi gidansu ta barsu.
---------
PAGE 60
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tun bayan dawowar Khadeeja gidan sau daya Baffanta ya shiga dakin Mommy ya sameta yayi mata sannu.
Yana zaune a parlor bayan ya dawo daga sallar tarawih Mommy ta shiga ta sameshi, ta zauna a gefensa suna kallon labarai a tashar Aljazeera tare. Bayan sun dan taba hira yace ‘Dazu Mustapha ya kirawoni yana duba Khadeeja, ya ma ce min idan an bude gari ranar asabar zai zo su tafi.’
Ta dan gyara zama ‘Ranar asabar fa kwana uku kenan, haba ai sai ta kwana arba’in.’
‘A’ah to ai ni na zata sun gama magana da ita ne a kan hakan.’
Ta jijjiga kai tace ‘Gaskiya dai basu yi wata magana ba don da kanta tace min tana so tayi arba’in din. Suna zuwa da na sa ruwan zafi nayi mata wanka ta ji dadin jikinta da kanta tace a barta tayi arba’in din. Haba, kuma haka za a mayar da ita haihuwar fari babu wani gyara? Sai kace ‘yar tsana.’
‘To ai naga bari ne ba haihuwa ba.’
‘To ai Baffan Nabila bari ya fi haihuwa wahala sosai ma, sannan kuma na fari ne haka za a bashi matar ya ma kasa daga mata a kwana arba’in din.’
‘To naga dai ai matarsa ce ko? Ina laifi, kuma ma ai shima ba zai ce bai san wadannan hukunce-hukuncen ba tunda ga yara nan har hudu an haifa masa.’
Ta sake gyara zama ‘Ku dai yi hakuri Baffa a barta tayi kwana arba’in ko akalla talatin, kafin nan ta ji daidai a jikinta sai ta koma.’
Ya daga wayarsa ya cigaba da dubawa yana cew a’To ai shikenan idan ya zo sai kuyi masa bayani, ni bani da matsala da hakan.’
‘Yauwa, ai lalacewar zamanin ba ta kai an daina wanka da gyara a haihuwar fari ba. Amma dai idan ya zo sai kayi masa bayanin idana kana nan tunda ka ga kai ya nema, gara ku cigaba da magana man to man.’
Yayi dariya yace ‘To babu laifi.’
Ya san halin matarsa da kishi, yanzu haka haushi taji shi Mustaphan bai kirawota ya duba Khadeejan ba ko akalla ya gaya mata zai tafi da Khadeeja ranar asabar tunda ya san iatace zata shirya Khadeejan amman ya kirawo Baffa. Jimawa kadan kuma fice ta bashi waje.
______
Shi da yara suka zauna suka gama shan ruwan sanna ya sa Afaf ta kwashe kwanukan, nan suka zauna suka cigaba da kallo suna wasannisu.
PAGE 61
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Har lokacin kwanciyar bacci babu wanda ya bashi matsala a yaran.
Ya tasa su a gaba ya raka su dakinsu domin suyi shirin bacci; yana shiga dakin zarni ya doki hancinsa. Ya dubi Afaf yace ‘Ba naga Ummi ta fitar da katifun nan ba? Me yasa suke zarni?’
‘Ta fitar Abba, sai da yamma sannan ta shigo da su gaba daya. Ban sani ba ko katifar Habib ce bata bushe ba don bamu san anyi fitsari ba sai wajen la’asar sanna ya gaya mata Shukra tayi masa fitsari bayan asuba da ka kwantar da ita. Shine aka shanya, to ina jin itace bata gama bushewa ba.’
Ya karewa dakin kallo, ko shimfida ba ayi ba a kan gadon don haka ya sa Afaf ta yi musu shimfida yayinda shi kuma ya wuce dasu bandaki don suyi brush. Nan da nan kowa ya shirya bayan sun fito sun kwanta ya cewa Afaf ‘Wai sai yaushe katifun nan zasu daina zarni ne?’
‘Nima ban sani ba Abba, kuma fa idan baka saka su sunyi fitsari da daddare ba haka gobe ma zasu sake yin fitsarin nan fa. Dama Anti ce kullum take tashinsu, Nasreen sau daya ita kuma Shukra sau biyu shi yasa basa yi a kwancen.’
‘To karfe nawa take tashinsu?’
‘Wallahi Abba nima ban sani ba, kawai dai tana tashinsu.’
Ya amsa sannan ya fito ya dawo parlo ya zauna; to shi yanzu ya za ayi ya san karef nawa zai saka su wani fitsari, gashi kuma ga dukkan alamu idan ya barsu suka cigaba da fitsarin nan a kwance to lallai gidan zai daina zaunuwa. To amma karfe nawa zai saka su? Watakila sai dai kawai idan ya tashi kwanciya bacci ya saka su shikenan.
Nan ya zauna a parlor din ya cigaba da kallonsa yana chatting, har ya sami Khadeejan ma online suka dan yi hira.
Basu fi awa daya da kwanciya ba ya jiyo kukan Shukra daga dakin, da sauri ya dire wayar da take hannunsa ya nufi dakin. Tana zaune a kan gadon tana ta faman kuka harda hawaye. Ya karasa ya zauna a kusa da ita yana cewa ‘Menene Shukra?
PAGE 62
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazi