ma yana kaita asibiti da makaranta, don cikinta nata na Hakeem irin mai masifar laulayi ne kamar bazata kai ba, ga miji baya kusa. Taiwo da Kehinde kaunar ‘yan uwantaka sukewa juna irin wadda ba duk ‘yan biyu ba.
A hankali Murjanatu taji numfarfashin Abdulrasheed a kunnenta, wani abu da bazata iya tuna (when last) ta ji shi ba, watakila tun farkon balagar su, lokacin da suna sakandire a kasar Japan idan Dade dinsu (mahaifinsu) ya hana shi hawa Doki ya janye shi daga bargar Dawakan Polo ya rankwasheshi yace ya tafi makaranta.
Haka zai yi ta furzar da numfarfashin bacin rai kamar mai nakuda, don baya iya kuka a rayuwarsa. Wannan numfarfashin (is a replica) na kuka a wurin Prince AbdulRasheed, “her very own Kehinde”.
Don haka lamarin ya daga hankalin Murjanatu fiyeda tsammaninsa.
Kiris ya rage Taiwo ma ta fashe da nata kukan na zallar kaico, da taya dan uwanta bakin ciki da kishi da Allah wadai, he is totally heartbroken a baka da zuci, lokacin da yake yi mata bayanin abinda ya faru dasu kwana biyu da suka wuce tsakanin sa da fiancée dinnasa Hasinah, da dan uwansu cousin dinsu kuma amininsa guda daya a family da ya janyo jikinsa yake amfana dashi wato (Adetokumbo).
Cewa yayi ya gansu suna irin sex din dabbobi akan gadonsa.
“What a betrayal!” Taiwo kanta a karshe (could not control her own tears), ta barsu suka zubo a kundukukinta. Sabida feeling din Prince nata ne. And she feels the pain din har fiye da shi, don ita da hannunta ta rike masa Hasinah ba da sanin maahifiyarsu ba da farko, don sun san bazata amince ba, har sai bayan ta fara nisa sosai da karatun sakandire ma a hannun Murjanatu sannan Nenne ta san da zamanta wurinta.
Zuciyar Murjanatu ta hau tafarfasa. Data tuna wacece Hasinah, da irin gatanta rayuwarta da Abdulrasheed yayi, kirjinta ya hau tururi kamar wuta ake hurawa.
Ta tuna wanene kaninta Prince Abdulrasheed, gatan da yake dashi da girman nasaba da matakin rayuwar da yake kai, amma duk bai duba su ba, sabida halin tawali’unsa irin na Nenne, ya zabi Hasinah a matsayin life-partner din da yake burin mallaka, against the wishes na mahaifiyarsu, ita kuma a matsayinta na mai son duk abinda Kehinde dinta yake so sai ta mara masa baya, ta taya shi son Hasinah a haka da zuciyarta daya.
Yau shekaru biyu kenan da suke ta takun saka da mahaifiyarsu a kan neman yardarta da amincewarta da aurensa da Haseenah, don Nenne ta kafa ta tsare bata boye ba, duk kirki irin nata da yawan taimakonta ga kowa kiri-kiri tace bata yarda Abdulrasheed ya aure ta ba, ba don komai ba sai don NASABA wani abu ce mai girma da muhimmanci a Aure. Amma a wannan lokacin, a wannan gabar, Taiwo ta san Prince support dinta kadai yake nema ba ingiza mai kantu da rura wuta ba.
Idan bata karfafeshi ba yau, waye zai zama karfinsa???
Nenne me zata ce in taji? Banda Allah ya kara? Ta dade tana cewa dasu bata kin Hasinah, amma tsintacciyar mage bata mage. Shi garin banza duk kyawunsa a farau-farau din banza ne.
Abin nufi wato mara tsarkin asali da kyawun nasaba ba duka keda tsarki ba. Shiyasa har gobe ba’a yi auren ba, ake ta jan lokaci. Don neman yarda da albarkar Nenne.
Ashe da rabon zancen Nenne zai tabbata gaskiya tun tana raye kuma tun gabanin cikar alkawarin dake tsakaninshi da Haseenah?
Taiwo ta kara fada a fili cikin girgiza kai “lallai tsintacciyar mage bata mage”. Kuma “Garin banza a farau-farau din banza yake karewa!”.
A tunanin ta Hasinah zata dubi maraicinta da daga darajarta da Abdulrasheed yayi a tsakanin mata tsararrakinta, musamman fiddota da yayi daga gidan marayu na garin Ambursa ya dauketa cikin mutunci ya kaiwa ‘yar uwarsa, ta yi sakandire ta ‘ya’yan gata, kafin daga nan ya kawota kasar Japan, yasa a makaranta, cikin ire-iren marayun da yake ponsoring scholarship dinsu a kasashen waje ba wanda ya kawo jikinsa wato inda yake zaune sai Haseenah, a tunaninta ko wannan ya isa yasa Haseenah ta tsayar da soyayyarta da sha’awarta da hankalinta akan sa shikadai, ta zame masa matar rufin asiri, ba kamar sauran ‘yammatan da ke haukar son shi don wasu kyale-kyale nasa ba, kamar kasancewarsa “basarake” kuma “celebrity”. Sannan gashi “Handsome Yoruba Demon” da shaidanun matan Africa dake kasashen ketare ke rububi don son sheke aya dashi kawai ba.
Ta dauka Hasinah zata barranta kanta daga masu neman soyayya ta watsewa bayan shigarta Jami’a, ta dauka Haseenah zata zama mai kamewa data iyawa maraicinta, ta dauka zata tsaya ga matsayin da Allah ya bata na fiancée din da Abdulrasheed ya yarda zai aura da zuciya daya cikin dimbin matan dake son shi da suka fita gata da kyawun nasaba, ko don kasancewarta musulma kuma bahaushiya, ashe kame kai ba daga yare ko kabila yake ba, saboda kyawun surar dan uwanta ma kadai ya ishi duk wata mace mai lafiya da dogon buri akan samun miji na nunawa sa’a tinkahon duk da zata yi a kan kowanne da namiji.
Taiwo ta zabi su bar maganar nan a tsakaninsu. Suka binneta a