A ganinsa yana baiwa kowanne lokacinsa yana kokari kwarai wajen kiyaye sallah a duk inda ya samu kansa. In akayi la’akari da irin schedules dinsa. Yana irin nasa kokarin a ganinsa.
“Magana ta domin Allah, Hammansu, ka maida kan ka kamar wani tsuntsu mai tashi sama kan fiffike, yau baka nan gobe baka can duk don hawa Doki?? Ni menene a cikin hawa doki ne? Ka ki tsugunnawa a wuri guda ka fuskanci rayuwa ta reality. Saboda Allah yaushe rabon ka da zuwa aikin Hajj don sauke farali balle umarah da take sunnah?
A tunanina duk wata daukaka, ko suna da kake nema cikin wannan sana’ar ina ganin zuwa yanzu daka mallaki kofunan Zinare sau ba adadi a sanadinta, in ban yi kuskure ba kofunanka sun kai biyar, ko shidda, ina ganin ai ka gama samun daukakar Polo kuma Hammansu.
Ko tunanin aure da aje iyali baka yi wanda shine wajibinka a rayuwa ta hakika kuma mai ma’ana ga dan adam, ba don komai ba sai don saboda hawa doki ne kadai a ranka, ka manta cewa harka fita shekarun kuruciya da jimawa ka shiga na girma, don ma dai bakayi kama da shekarun ka ba; you are still looking fit and healthy”.
Nenne ta kara kwantar da murya yadda dole dan nata ya tausaya mata, tace “Abdulrasheed ko tausayina baka ji, duk faccalolina sun ajiye jikokin ‘ya’yansu maza ni ko daya babu, ba don Taiwo ta bani ba, jikoki ba da saidai kowa ya riga ni tarawa, har wadanda sukazo a bayana, ga maganganun nan marassa dadi da duniya ke yi akan ka suna dawowa kunnenmu, haka ‘yan uwan ubanka suma suke yimin irin tasu tijarar a kanka, suna ganin ni na hana Ubanka kara aure har tsufansa, haka zai mutu da mace daya kamar rai sai kace auren zobe, kai kuma dana haifa mun daure maka gindi kana yawon tambada da lalata a duniya ka ki cika Sunnah, kana gudun aure wanda yake sunnar Annabi SAW.
Ka ki ko tsayawa kayi tunanin ya kamata ace a wannan matakin na rayuwarka kana da yara lafiyayyu har guda uku ko hudu.
Yau dai tunda Doki ya kusa hallaka ka kana ji kana gani, ina ganin ya kamata ka hakura dashi haka Kehinde! Babu sauran alfanu kuma a cikin hawansa”.
Prince AbdulRasheed ya muskuta ya gyara kwanciyar sa cikin jin azabar zafin ciwo irin na hadewar kashi, yace.
“Nenne bana so ko kadan kike sakawa kanki damuwa akan abinda at least kin riga kin san bazan iya bari da sauki ba.
Polo ya zama wani bangare na jikina Nenne, ina yi ne kawai don jin dadina da biyan bukatar sha’awata ga wasan Polo, amma ba don tara kofuna ba, yana debe min kewa yana hanani tunani yana kuma hana ni damuwa da komai, ba don neman wani abu kuma nake Polo ba ko da can balle yanzu da nake da aikin yi kwakkwara, don haka banaso kina damuwa da ance-ance din mutane wadanda basu da gadonka. Su mutane ai al’adarsu ne damuwa da abinda bai shafesu ba.
Abinda ka kwashe rabin shekarun rayuwarka kana yi yana da wuyar bari a dare daya kuma farat daya Nenne. Kimin addu’a, idan inada rabon barin hawa Doki in bari a hankali.
Nenne nifa zan iya ajiye aikina na refinery dungurungum! In rungumi wasan Polo shikadai.
Idan Doki shine ajalina haka Allah ya kaddara min Nenne”.
Yayi dan shiru yana dan haki, na zafi da zogin ciwon karaya, kafin yace “Nenne tun shigowarki bakiyi duba da halin ciwo da nake ciki ba, sannan ko jajen raunin da SAHEEB yaji baki yimin ba kin hau ni da fadan rashin aure anya Nenne?
Ki godewa Allah da ban zarce ba, na barki da ciwon rashina bana rashin aurena ba.
Kimin addu’ar samun sauki da gaggawa kinji Nenne na, ki daina damun kanki akan abinda banida rabo a cikinsa, ki roka min tsahon rai da lafiya mai amfani mu rayu tare, yafi min rayuwa da wata mace, tunda ba wani abun kunya na ke yi a yawon hawa Dokin nawa ba, sha’awa ce kawai, hobby na ne kawai yin wasan Polo.
Amma ba haka kawai rana daya kice lallai in bar abinda nafi so a rayuwata ba, wai don tsautsayi ya gitta min wand aba yau farau ba, kuma mutane suna maganar banza a kaina da ke, ina ruwana da maganar mutane?
Ko an gaya musu inada business da mutane su yabe ni ko su zage ni?
Aure ra’ayi ne, kuma banida ra’ayin yinsa a yanzu, tunda dai auren nan Sunnah ne ba farillah ba”.
Nanne sai ta zama speechless, ta rasa me zata ce masa kuma, duk ta inda tabi don Kehinde ya gane damuwarta da ciwon ranta akan rashin aurensa bazai gane ba, ta yarda kuma babu abinda zai sa AbdulRasheed barin Polo, idan wannan karairayewar da ta sameshi yanzu, basu saka ya barta hakannan ba.
Ta kuma yarda bashi da niyyar yin aure nan kusa, aure baya ransa kwata-kwata, baya cikin burikansa da fatansa na gaba, burinta na samun jikoki daga jikinsa, bata san ranar da Allah zai dubeta ya cika mata shi ba.
Wayar Murjanatu ce ta katse tunanin Nenne, ta boye dan guntun hawayen da ya tsatstsafo mata. Hankalin sa kacokam ya koma kan waya da Aunty Taiwo dake ta koka jin abinda ya sameshi ta waya tana zata taho itama yana ta zauna ai ya ji sauki, yana lallashinta da taushin murya, yana gaya mata ta san dai ba yau ya fara faduwa a Doki ba