bai kula ta ba, itama haushi yasa ta dauke kai daga kansa tai kwanciyarta, kankace me bacci yayi gaba da ita.
Kwanciya yai ta saitinta yanda yana hangota daga kan gado, ya kura mata ido, what are u to me?
Gani yai tayi juyi ta juya mai baya.
Mikewa na ga yayi ya dau pillow dinsa ya kwanta akan kujera yanda zai ganta dan kusa da kujerar take shimfida.
Ajiyar zuciya yai ya kalli bargon data shimfida yace "wannan bazai sata ciwon baya ba? Kullum kwana a kasa? Gata ba jiki ba?"
(Nikuwa nace waye ya sata🤨)
Ya dade a haka yana kallanta har bacci ya daukeshi.
Yauma Alhamdulila bai farka da ciwo ba, wajen asuba ya farka, da sauri ya mike yana mamakin kansa anan ya kwana? Ahh wai Hassan hankalinka daya kuwa?
Alwala yai sannan yazo kusa da ita, ya saba sa kafa ya tasheta yau sai gani nai ya sunkuyo yasa hannu yadan bugi kafadarta tare da cewa "Jalila?"
Idanu ta bude cikin bacci ta kalleshi, mikewa yai.
Ta mike itama tai alwala...........
Tunda ta tashi take jinta ba dadi, ba sabon abu bane tasan period dinta ne ya kusa, ita kuma gashi duk sanda zatai al'ada sai tasha azaba na ciwon mara, a gida Goggo sai ta sata tasha dauri, ko ta siyo panadol......
***********
Inna ce tasa aka kira mata dady, yana zama mumy ta shigo taja ta zauna.
Inna tace "Fatima meye hakan? Magana zamuyi."
Mumy tace "kome zakuyi kuyi agabana, sannan nima magana nazo fadamiki."
Inna ta kalleta tace "maganar me?"
Tace "kiba Abubakar mukamin Chairman na company ke kiyi resigning, dama ai kin dade kina cewa zaki bani ke kuma ki sauka."
Inna ta kalleta cikin tashin hankali sannan ta kalli Dady wanda shima yai alamar wai mamaki, tace "Abakar kai ka zigata?"
Da sauri Dady ya kalleta yace "Menene hakan? Ce miki nai inasan shugabanci na company din? Meyasa kike neman sa Inna taga kamar nine nake saki abu? Banasan irin wannan abun."
Mumy ta kalleshi tace "Dadyn Yasmeen."
Ya hade rai yace "Taya zaki yanke hukunci ba tare da kin sanar dani ba?"
Tace "gani nai...."
Inna ta kalleshi lalai yaran nan me? Ce miki akai inasan shugabanci?????
Tai wani murmushin takaici.......
#Oneluv💕
[12/7, 9:53 PM] El-hajj: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*48*
Ummy ce ta kalli Jalila tace "Jalila lafiya? Naga tau kamar bakyajin dadi?"
Tace "lafiya ta kalau Ummy."
Ummu tace "da ina tunanin ko in dau Goggo da Ameera muje dakanmu mu siyo kayan gidan muje a saka, kamar zaifi dan nasan halin Hassan bazai shiga gun kayan ba, kinga kuma ke kadai abin bazai yiwu ba, sai da babba."
Jalila tace "to Ummy."
Ummy tace "ko kinfiso kije da kanki? Ko mu tafi tare?"
Da sauri tace "a'a wlh Ummy hakan yafi, ni me na sani a wannan harkar?"
Ummy tai murmushi ita kuma bataso subar Hassan shikadai dan Abba ya fita duba wani aiki.
Jalila tace "me za'a dafa da rana?"
Ummy tace "komai ma duk abinda miki."
Jalila tai murmushi sannan tace "to Ummy nagode Allah ya saka da alkairi."
Ummy ta kalleta cikin kulawa tace "Hassan fa?"
Jalila tace "yana daki."
Ummy tace "nasan yana daki ai haryanzu bai sauko ba?"
Jalila tace "Ummy kema harkin gane? Ni na rasa me namai."
Ummy ta guntse dariyar dake neman zuwa mata tace " da alama dai kin mai babban laifi tunda har nima na gane."
Jalila tai ajiyar zuciya tace "na kasa gane me namai, kuma shima ya ki fadamin."
Ameera da ta fito tasa dariya tace " ba kunya?"
Jalila ta kalleta sannan tai saurin mikewa, sai yanzu ta fahimci bai dace ba.
Ummy tasa hannu ta rikota ta makama Ameera harara tace "to uwar sa ido, menene damuwarki? Ni bana sirikanta da ita 'ya ta ce."
Ameera ta kara yin dariya tace "hmm nayi shiru ai."
Ummy ta kalleta tace "kicema Goggo ta shirya zamuje wani guri."
Ameera tace "ina zaku bani?"
"Ko shirya dake zamuje kema, in muka sai kayan farko sai ke da Lantana da Goggo akaiku gidan ni da Sageer sai mu karasa siyan abinda ya kamata."
Ameera tace to, tai ciki da sauri.
Haka suka shirya Jalila na kusa da Goggonta, Goggo sai tambayarta take wai ina zasu? Itakam Jalila cewa kawai take nima ban sani ba Goggo.
Haka suka fito Sageer ya daukesu a mota, Jalila ta baishi da kallo duk ya canza da dai ba haka tasan Uncle ba, mutum ne faran faran dasan tsokana, yanzu kuwa ya rage sannan duk yadan rame.
Tana tsaye har motar tasu ta bar gidan sannan ta dawo ciki.
A falon kasa tadan kwanta dan mararta ciwo take mata daurewa kawai takeyi, mikewa tai can ta hau sama dan tana san shiga toilet.
Hannu tasa ta bude kofar dakin dakin ta shiga, yana zaune a kasa yana cin abinci da alama baima dade da tashi ba.
Tana shigowa ya kalleta, itama kallansa tai ta tsaya sannan tace "Yaya ka tashi?"
"Umm, dazu." Ya fada idansa na kanta, ta dan tsaya kafin tace "hmm su Ummy sun fita tare da su Goggo."
Yace "okay."
Tadanyi shiru kadan sannan tace " duk tare suka fita."
Yace "nagane, kina nufin daga ni sai ke kenan ko?"
Tace "hmm can gidan zasu."
Yace "duk na fahimta."
Juyawa tai ta nufi toil