kadan tace "Sir nayi laifi."
Bai ce komai ba sai wani kallo da yake mata, gana kokarin b'oye abinda ke ransa, dan bai manta ita din dalibarsa bace.
Ta fara wasa da hannunta sannan tace "Lemarka jiya ta samu matsala."
Yace "ta samu matsala ko dai ba'a damu da ita ba an lalatata?"
Da sauri tace " ba haka bane, Allah iska ce ta dinga bankareta....."
Yanayin fuskarsa ne ya canza zuwa kulawa, yace "ba dai abinda ya sameki ko? Are u okay?"
Ganin yanda ya damu da ita yasa taji ta kasa cewa komai, yanda take kallansa ne yai saurin juyawa ya kalli daliban dake ta shiga makarantar yace " Ki wuce cikin makaranta."maganar ya karasa tare da juyawa yana kallan mashin din.
Jalila ta fara tafiya a hankali tana mamakin kulawar da yake nuna mata wanda ke kokarin sa zargin so a zuciyarta, anya kuwa? Karfa zuciyarta ta raya mata abinda ba haka ba, Uncle Sagir yafi karfinta, dan mata dayawa na sanshi, sannan da alama dan gidan wani ne duba da yanayin yanda yake zuwa wani sa'in a mota.
Wata zuciyarce ta ce mata ina ruwan so da wannan?
Juyowa tai bayan tayi tafiya mai nisa, ga mamakinta gani tai idanunsa na kanta, suna hada ido yai saurin juyawa, Jalila ta juya cikin yanayin jin kunya.
**********
A company dinsu Dady kuwa suna isa sukaga mutane ancika a waje.
Da sauri sukai parking Dady ya fito cikin tashin hankali, suna ganinshi sukayo kanshi.
Mumy na gefensa, cikin tsantsar tashin hankali yace " gaba daya kayanda muka adana sun lalace?"
Cikin damuwa yace " Muje ka gani."
Store din da suke adana dukan kayan aikin da sukeyi ya bude.
Store din acike yake da kayan ma'a dana na abinci.
Gaba daya hankalin Dady ya tashi dan kana gani kasan lalai lalata musu akai.
Juyowa yai yace " How can this happen? How......."
Mumy ma hankalinta ya tashi ta kalli Dady tace "Yanzu ya zamuyi? Gashi zuwanka Abuja munyi signing da Al-Company zamu aika musu da kayan cikin satin nan."
Wata zuface ta karyomai yace "Muje gida mu sanar ma Inna, sai muyi tunanin mafita, dolene mu san yanda zamuyi kafin nexweek."
Hankali a tashe suka juya gida.
Inna macece wacce tasan kan kasuwanci, dan company dinsu ya bunkasa ne harda tsananin iya kasuwancin ta, shiyasa mijinta yake girmama kalamanta sannan takeji da kanta itama.
Har Allah ya mai rasuwa, ta dade tana juya company din da kanta duk kuwa da ganin Dadyna iya nasa kokarin a karkashinta,har sai dataga girma ya kamata tana bukatar Hutu sannan tabar Dady yakejan ragama.
Inna wacce yanzu ne ta maida sunanta haka, dan da kowa Hajiya yake kiranta, yanzun ma Sultan ne ya sa mata hakan har kowa ya koma kiranta haka a gidan, amma daga ta fita sai dai kaji ana Hajiya.
Tai shiru kafin tace "nawa ne a account dinmu?"
Yace "Hajiya mun kwashe rabin kudin mun sai kayan aiki, ba nakawo miki budget din ba?"
Hannu tasa ta shafi fuskarta tace "Kudin bazasu kai musai wasu kayan ba kenan?"
Kasa yai dakai yace "Gaba dayan mun gama shirya plan dinmu banaji ko kwata zai kai."
Ta dade batace komai ba da alama nazari take kafin tace "Sai dai kenan mubi last option din da banaso."
Yace "Loan?"
Tace " dole zan duba a cikin mutanen Alhaji da nawa wanene na amana sai musan yanda zamuyi, either mu samu loan ko kuma yayi investing."
Kai ya jinjina sannan yace "bari a kira board meeting sai a tattauna."
Tace "No ka bari sai zuwa gobe in na samu wanda zai tallafa mana."
Yace " To Hajiya."
Nan ya mike ya fita, wani karamin diary ta d'auko ta shiga duba sunaye tana auna mutane.......
#Oneluv๐
[08/10, 19:18] โช+234 816 365 0557โฌ: ๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*No 5*
Yau a staff room yai shiru yana tunanin yanda zaiyi, ya dade yana tunani dan baisan ma sanda wani staff yazo kusa dashi ba yace "Sagir mu mun wuce sai gobe in Allah ya kaimu."
Kallanshi yai cikin mamaki sannan ya kalli agoggon dake jikin bango, lalai har an tashi da kusan minti goma ma.
Yace "To Sai goben."
Nan ya shiga hada kayansa shima, a tsaye ya ganta a inda ta saba tsayuwa, ya dade yana kallanta sannan ya karasa kusa da ita yace "Malamar jira."
Kallansa tai sannan ta sunkuyar da kanta tana murmushi dama yanzu take tunanin bata ga fitarsa ba.
Jitai yace mata "D'an zo."ya fada tare da fara tafiya, cikin mamaki take binsa har suka shiga wani class.
Zama yai a saman desk sannan ya mata alama data zauna daga kujerar dake gefensa kadan.
Bata musa ba ta zauna, sai daya d'an yi shiru na wasu dakiku kafin taji yace " Jalila!"
Yanda ya kira sunanta ne yasa taji wani abu yar wanda ya hanata amsawa sai kallansa datai, yana kallanta yace " labari zan baki."
Nan ma batace komai ba sai kallansa data sake yi, murmushi yai sannan yace "akwai wani sokon abokina da ya taba ganin wata yarinya tun last year, ya taho shida kanwarsa zasuje gidan yayar mahaifiyarsu, sun tafe sai kanwar tasa tace "Yaya dan Allah mu tsaya musai maganin ciwon