Tace "meyasa kakesan sani?"
Yace "Hmm kawai, saboda sai naji ne zansan abinda ya dace nai."
Hannunta ta nemi janyewa tana cewa "me ya faru dakai? Duk sanda kake abin nan kamar wani abu kake tunani."
Shiru yai bai bata amsa ba, kafin can yace " izinki nawa?"
Tace "mene?"
Yace "tambayarki nai, so nake nasan karatunki, na kula kamar bakiyi nisa ba."
Tadan sosa wuyanta da dayan hannun tace "bankai izu ko daya ba, a gida Goggo tadan koyamin na sallah."
Idanu ya kura mata, wanda yasatai saurin juya kai yace "bakyajin zafin mahaifinki?"
Tai shiru kafin tace "inaji, inaji sosai da har wani sa'in ganinsa ma banaso."
Yace "kenan ko me ya faru bazakiji haushi ba?"
Tace "me zakamai?"
Mikewa yai daga kan cinyarta sannan ya saki hannunta yahau kan gado....
Da sauri ta taso tace "me zakayi?"
Yace "bakomai, fada kawai nai."
Jalila ta kalleshi alamar rashin gamsuwa.........
********
Dady kuwa yana saukowa daga gun Inna ya shiga daki kawai ya hau hada kayansa, Mumy ta shigo da sauri zatai magana taga yana hada kaya, a rikice ta rike hannunsa tace "Dear menene?"
Ture ta yai yace " menene? Da alama karshen zamana dake yazo."
Da sauri ta rungumeshi tace "menene? Kafi kowa sanin bazan iya rabuwa dakai ba, Inna ce? Itace?"
Yai shiru wai shi a dole ransa ya baci.
Da sauri ta fito ta nufi dakin Inna da gudu rai a bace.........
#OneLuv๐
๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
โote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*45*
Da karfi ta banko kofar dakin Inna, lokacin Inna na zaune tasa hannu tayi tagumi tana tunanin abinyi, yanda Mumy ta banko kofar ne yasa ta zabura ta kalleta tace "Lafiya?"
Mumy cikin bacin rai ta zauna a gaban Inna tace "Inna so kike kiyi ajalina?"
"Ajalinki kamar ya kenan?"
Tace "in ba so kike in mutu ba taya zaki nemi halakamin aure? Sanin kanki ne yanzu kinsan bazan iya rayuwar ba Abubakar ba, a da ma da 'ya'ya basu hadamu ba na kasa rabuwa dashi bare yanzu."
Inna ta katseta cikin fada tace "me ya fadamiki?"
Tace "ba damuwa ta bace da duk abinda kike tunani sai dai kiyi abinki ke kadai, dan wallahi bazan bari wani abu ya sameshi ba, in kuma so kike mu bar miki gidan to....."
Mamaki ya kama Inna ta kalleta cikin wani yanayi tace "Fatima ni kike fadama haka? Ni wacce ma sadaukar da komai dan ganin farincikin ki?"
Cikin masifa tace "kika sadaukar dame? Me kika sadaukar? Duk abinda kikeyi ba saboda kanki kikeyi ba? In har saboda nine ai da kin daraja Abakar kin bashi company din kamar........."
Marin data kifa mata ne yasa Mumy yin shiru, ta kalleta tare da rike kuncinta.
Inna ta kalli Hannunta dake rawa, dan ita kanta batasan ta mareta ba, cikin dana sani tace "Fatima......"
Mumy ta mike tsaye tana kallanta, hawaye sun cika mata ido tace " in har bakyasan in bar gidan nan ki ajiye duk abinda kike shirin yi." Ta juya tanaji tana kiranta bata amsa ba tai waje.
Inna ta bita da kallo jiki a sanyaye.....
Shikam Dady tana fita yai wata dariyar mugunta yace "Inna i am sry sai dai kin riga kin makaro akaina 'yarki da kikafiso a duniya zata iya juya miki baya."
Yanajin alamun bude kofar ya shiga kokarin zuge jaka, Mumy na shigowa ta sa hannu da karfi ta fincike jakar sannan ta rungumeshi tace "Dadyn Yasmeen me yasa baka tunani na in zaka aikata abu?"
Yace "tunanin naki ne yasani yanke wannan hukuncin, taya zan zubarma kaina mutunci? Bayan nasan ina zubar da mutunci na naki na zubar? Da ace kome zai faru zai tsaya akaina ni kadai bazai shafeki ko yaranmu ba wlh ba abinda bazan iya ba, amma ta yaya zan yarda in zubar da mutuncinki dana 'ya'yanmu."
Dagowa tai tana kallansa tace "to kamin alkawari ko me zai faru bazaka sake tunanin rabuwa dani ba."
Yace "na miki, yanzun ma ba'a san raina nake shirin tafiya ba."
Ta kara kankameshi tace "barni da Inna bazan kara bari ta wulakantamin kai ba"
Ya shafa kanta yana wani murmushin mugunta yace " taya zan yarda na zama sillan fada tsakaninki da mahaifiyarki?"
Tace " ba kaine silla ba dan dama na gaji da yanda take ma kamar wani bawanta."
Nan ya sumbaceta a kunci yace "i luv u Zarah."
Ta sakarmai murmushin so......
Nace ansha kauna๐
Inna kuwa Mumy na fita ta ture littatafan dake kan tabir din gabanta cikin takaici tace "Abakar how dare you!"
Kwafa tai tace " kana tunanin ka samu abinda kakeso? Inji wa?"
Ta sakeyin wata kwafa........
********
Zama tai a kusa dashi a kan gado yana kwance yana tunanin Zaliha, ji yake zuciyarsa kamar zata fashe da rashinta.
Ganin baimasan ta zo bane yasa tasa hannu ta tabashi.
Kallanta yai sannan ya kakaro murmushi yace "Yaushe kika shigo?"
Tace "me kake tunani?"
Kallanta yai jiki a sanyaye, murmushi tamai sannan ta kauda kai, a hankali yace "I am sry, i am really sry."
Kallansa ta sakeyi tace "me kake tunani game da mutanen nan?"
Ya mike ya zauna yace "amsar kudinmu