aga ta fasa, kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa tace "nagode." Kawai tace ta juya ta hau saman.
Tsayawa yai yana kallanta cikin tsananin tausayi, har saida tai kwana sannan ya juya zuwa dakinsa, yana shiga ya zauna a bakin gado yana tunani, haka rayuwarta take? Shiyasa ashe ake barinta a makaranta ita kadai? Shiyasa sukasata a government?
*******
Ummy ta taso tazo kusa da ita, suka fita tare, ina saurayin Jalila? Ta tabbatar Jalila.......... tunowa datai a inda tasan Sageer ne yasa ta kalli Ummy da sauri tace "ya sunan mijin Jalila?"
Ummy tace "Hassan!"
Goggo tace "wanda na gani dazu fa?"
Ummy tace "Sageer? Kaninsa ne."
Goggo tace "kaninsa?"
Ummy ta daga kai alamar eh, Goggo a ranta tace "to ko ba shi bane?"
Dakin Ameera ta kaita sannan tace "kici abinci ki kwanta, dan Allah karkiyi tunanin komai, Jalila yanzu 'yatace bazan kara bari wani abu ya sameta ba, sannan mu zamu san abinyi, ke dai ki kwantar da hankalinki ko dan lalurarki."
Goggo ta riko hannun Ummy tace "Nagode, nagode har bansan iya godiyar daya kamata nai miki ba."
Ummy tai murmushi tace "muma mungode, da kika fahimcemu, yanzu sai kisama auransu albarka."
Tace "insha Allah."
Nan ta shiga ciki.....
Ummy ta bita da kallan tausayi.
Jalila kam kamar zata shiga ciki sai kuma ta fasa, zama tai a falo kawai tana kuka ko kwanwutar bata kunna ba.
Shima zama yai a kasa ya kwanatar da kansa akan kujerar dakin, wace irin rayuwa yarinyar nan tai? Amma duk da haka akwai laifinsa a ciki, ya tabbatar dabadan shi ba da baza'a mata auran dole haka ba, wadan nan tunani sune suke tayimai zirya a ransa, tarinta yaji hakan yasa ya kalli kofar falon.
Mikewa naga yayi ya jingina kansa da jikin kofar, sheshekar kukanta yaji wanda yasashi rufe ido cikin tausayawa.
Jin kukan yake har zuciyarsa, a hankali ya bude kofar.
Dayake makunin fitilar falon a kusa da kofar take kawai sai ya kunna ta.
Haske ne ya baibaye falon, da sauri ta dago.
Jingina kansa yai da jikin kkatangar falon yana kallanta tare da sa hannunsa na hagu cikin aljihunsa.
Kallansa itama takeyi, sun dade a haka kafin ta sauke idanunta kasa.
Yace " yau ma hobby din naki ya motsa ne?"
Ta kalleshi da idanunta da suka sha kuka, yace "a rana kuka nawa kikeyi?"
Baki tadan motsa tanasan magana, yace " in zakiyi kuka kiyi a gurin daba kowa, dan ni ba hobby dina bane sauraransa."
Ya juya bai rufe kofar ba ya zauna akan kujera, me yasa yace haka? Shi dayaje dan ya lalasheta?
Mikewa yai yai sallar Isha'i, ganin batada niyyar shigowa yasa yaki mikewa daga kan sallayar, yana jiranta.
Kofar yake lekawa, yaga ba alama.
Pillow ya janyo yasa kansa akai yana kallan kofar.
Abincin su ya kalla, bataci abinci ba, shiru yai yana tunanin shigowarta.
Yana nan a kwance har karfe 10, baisan sanda bacci yai gaba dashi ba.
Jalila kam bayan ya juya kawai ta kwanta akan kujerar tana yan mitoci, kasan baka damu da hawayena ba me yasa dazu kazo? Nikam Yaya me yasa baya magana mai sanyi? Tadan turo baki ta kwanta tana tunanin rayuwarsu.
Batasan bacci ya dauketa ba, sai karfe 11 ta farka, batai isha'i ba ya akai bacci ya dauketa?
Da sauri ta sauko daga kan kujera ta nufi dakin, a kwance ta ganshi a kasa, batai mamaki ba dan taga yanayi, kawai ta wuce toilet.
Tai alwala tazo tai sallah, jitai cikinta na karar yunwa, ta zo ta bude abinci zataci, gani tai ba alamar taba abincin, baici abincin dare ba kenan?
Kadan ta zuba a plate ta faraci.
Lomarta uku taji kakarinsa, wani sankamewa yakeyi, da sauri ta ajiye abincin ta matso inda yake.
Gaba daya ya sai juye juye yake, yana girgiza kai alamar a'a, ga zufa tanata keto mai.
Hannunsa ta riko tana tabashi, Yayah! Yayah!
Gaba daya ba alamun yanajinta, kansa ta kwantar a kan cinyarya dan murkususun dayake yasa kansa ya sauka daga kan pillow din, tasa hannu ta rike kansa dayan hannun kuma tasa a saman kirjinsa tana dan tabashi tare da kiran sunansa.
Can kuma sai tadanyi kulhuwalahu da falaq da Nasi sai tadan tofa mai.
A hankali taji ya daina motsumutson.
Idanunta na kansa ya ciciko saboda da tausayinsa, wannan wani irin abu ne ke damunshi? Me ya sameshi abaya?
A hankali ya bude idanunsa, daidai lokacin kwalarta ta zubo ta zubu saiti idanunsa, wanda yana rufe ido ta zubo a bayan idansa.
Idanunsa ya sake budewa ya kalleta, dayan hannun data rike kansa dashi ta saki ta share hawayenta sannan ta kalleshi tace "Yayah!"
Idanunsa ya lumshe yana kallanta kamar yanda take kallansa cikin sansanyiyar murya mai kamma da rada yace "sai yaushe ne zaki daina saurin kuka?"
Tace " kukan ne bakaso nayi?" Itama a hankali tai maganar tana kallansa.
Mamaki ne ya kamata dataga ya daga kai alamar eh, tace "meyasa?"
Ya dan girgiza kai kadan yace "ban sani ba nima, sai dai I don't like it."
Kallansa tai tare da neman zare hannunta daga kan kirjinsa.
Hannu yasa ya tsayar da hannu yana kallanta yace " yanzu kukan me kikeyi?"