ahaifinki amma kinki, kin dage sai dai mijinki yai, sannan yanzu kice me?"
Mumy tai kasa dakai sannan tace "Inna wai dan Allah sai yaushe ne zaki amince da Abakar daro bisa dari? Mutumin nan na miki ladabi wanda ko ni bana miki, sannan ya a sona san da ba wanda yakemin irinshi..."
Inna tai tsaki tace "ni tashi ki bani guri nasan mafitar data dace damu dan zamanki anan bakomai yake karamin ba sai bakin ciki."
Mumy ta mike tai waje rai a bace....
Inna tai shiru tana tunani kafin ta dau waya ta kira Abakar.
Yana zaune a falo Mumy na gefensa itada Yasmeen, Sultan na daki yana ganin kiranta gabansa ya fadi ya kalli Mumy yace da alama Inna tagama shawara.
Mumy tace "muje tare."
Yace "karki damu ki zauna bari naje."
Nan ya mike yai sama.........
**********
Inna ta tashi tayi wanka, Ummy ta kawo mata kayanta tace ta saka, dan itakam ta kula kayan dake jikinta da wanda aka dauko a leda san ba magana, itada Jalila ne sukaje BQ dan ganin yanayin gun.
Jalila ta kalli Ummy tace "Ummy kije ciki zan gyara."
Ummy tai murmushi tace "Jalila ko dai ince masu aiki gidannan sundinga kwana ne?"
Jalila tace "saboda me?"
Tace "da alama aikin gidan ya karu, sannan zai yi yawa, tunda akwai bangarensu ina tunani gwara mu tambayesu, in zasu dinga kwana to, in kuma bazasuyi ba kinga sai mu samo wasu."
Jalila tai shiru can tace " Ummy gani, ga Lantana ina tunanin ba wani abu."
Ummy tai murmushi tace "baki fahimceni ba kenan."
Jalila ta mata kallo mai alamar tambaya tace "ban....."
Ummy tai dan dariya tace "so nake kibama Hassan kulawa 80% dan na kula ina hanaki kula dashi."
Jalila da sauri ta juya tana tattare kaya dan kunya, Ummy ta sake dariya tace "ko nayi sankai?"
Jalila tace "a'a kawai ta cigaba da aikinta.
Ummy ta kalleta tana murmushi, Lantana ta kira suka gyara gun, Ummy tace "gobe sai a siyo gado da kayan bukata a sa a ciki, wai gadan ciki ya tsufa, da Jalila zatai magana Ummy ta harareta wanda yasata yin shiru.
Sageer kuwa a daki hankalinsa duk ya tashi tabbas Goggonta ganshi a lokacin dan har gaisheta yayi, to amma tagane tsakaninsu? Malam Sagir ashe da raban zan ganka.
Kalaman Goggo ne suka dawo mai, ajiyar zuciya yai cikin tashin hankali yace " ba zama bane ya dace dani."
Mikewa yai ta budo kofar dakinsa a hankali ha sako kai, yana leke.
Bakowa a falon, komawa yai ciki ya zauna yana tunanin abinyi, can ya daure ya fito a hankali yai falo, Ummy na zaune rike da littafin addu'oi ya shigo.
Ta kalleshi tace "Sageer fitowarka kenan, tun rana sai yamma?"
Yace "Ummy ina matar Yaya?"
Tace "Jalila? Tana BQ suna aiki, ta dage sai na taho, ya akai? Nemanta kake?"
Yai murmushin dole sannan yace "eh, bari naje can."
Ummy tace "to, amma Sagir karka tambayeta maganar mahaifiyarta, da magrib in anyi sallah za'a zauna a falon Abbanka."
Yace "to Ummy sannan yai waje.
Tana kwashe shara ya tsaya a bakin kofar yana kallanta.
Kallansa tai sannan ta matso inda yake jiki a sanyaye.
Kallan dakin yai, ya kalli Kofar Toilet inda Lantana ke wankewa.
Yace "Jalila!"
Yace "Uhmm"
Shiru suka danyi dan they are uncomfortable in suna tare ba kamar da ba.
Can ya daure yace "Goggonki, sanda mukaje asibiti....."
Sai a lokacin itama abin yazo mata, ta kalleshi da sauri tace "Ta ganka ko?"
Yace "kin manta har gaisawa munyi?"
Tai shiru tana kallansa, yace "Jalila, zaki iya mata magana? Dan banasan kowa yasan abinda ya faru a baya."
Jalila ta kalleshi tace "ince me? Ince Goggo yayan Uncle nake aure? Ko ince Goggo karki fadama kowa irin san da nakema Kanin mijina? Ko ince Goggo da naso Uncle ashe kanin mijinane?"
Yace "Jalila ya kikesan juya maganar da na fada ne? Me yasa bakya yima kalamai na kyakyasar fahimta?"
Idanunta ne suka ciciko tace "Uncle ni to ya zanyi? Me zance? Kamar yanda kake tsoron matsala ta afko a dalilinka, matsalar da zata sa hankalin iyayenka su tashi ni kaina a yanzu bana san ace nice silar wargaza farinciki Ummy da Abba, dakai kanka da yayanka, Uncle bansan....."
Kasa karasawa tai saboda kuka dake neman zuwa mata dan muryarta ta fara rawa.
Sageer yai shiru yana kallanta cikin tausayawa yace "Nafahimceki Jalila, na kuma gode da kaunar da kikema Family na, Please ko Goggonta tambayeki kawai kice mata sunane yazo daya, mu barshi kawai a haka."
Ta daga kai, kawai dan batasan itakam me zata kuma cewa ba...
Bayan sun gama aiki tai wanka a toilet din ta maida kayan jikinta ta hau sama.
Yana kwance yana bacci ta shiga a hankali ta dau kaya ta saka, sannan ta matso kusa dashi ta sa hannunta akansa, jin ba zafi yasa tai murmushi.
Da alama yau ma ciwon nasa da sauki, dan bacci yake hankalinsa a kwance.
*********
Bayan magrib kuwa Ummy ta kalli Jalila bayan sun gama girki tace "Jalila inkin kaima Goggon ki ajiye sannan ki kaita falon Abba zamuyi magana."
Tace to, sannan ta dauki Abincin Goggo, tana shiga dakin ta zauna kusa da Goggo tare da kwanciya a kafadar ta tace "Goggona!"