yai kallan zargi, Abba yace "Hafiz Please ka barni tukunna."
Bai kara jiran yayi wata magana ba ya katse layin, Hassan ya kalleshi kamar zaiyi magana sai kuma ya gaisheshi.
Abba ya amsa yace "Hassan."
Kallansa yai yace "kai da wanene haka?"
Yace "business ne ba wani abun ba uban yan zargi."
Hassan ya juya kai sannan yace "me kaba iyayen Yarinyarnan a maimakon auranmu?"
Abba ya kalleshi cikin mamaki yace "Hassan menene?"
Hassan yace "bakomai, kawai dai so nake nasani, dan na tabbatar give and take kukai da rayuwar ta."
Abba yai shiru kafin can yace "Bakasanta ne ko me? Ko wani abun ne ya faru?"
Shiru yai baice komai ba, kamar kuma zai saie magana sai ya juya zai tafi, Abba ne yace "Company dinsu ne ya ke neman yin Bankrupt shine na taimaka musu."
Hassan ya kalleshi sannan yace "yarinyar fa? Have u take care of her?"
Abba yace "kamar ya kenan?"
Hassan ya kalleshi yace "Abba ina dai sone a komai zakayi ga dinga tuna wacece Ummy a garemu."
Abba ya kalleshi yace "Hassan just pray for me, wlh nikaina bansan meke damuna ba."
Hassan yai shiru yana kallansa, Abba yacigaba "yanzu zan fada mata abinda ke faruwa itama, Hassan kafi kowa sanin family na are above komai na rayuwata ciki kuwa har da ni kaina, kasan yanda zan iya sadaukar da komai saboda su, sai dai i feel like there is definitely something wrong with me, na rasa yanda zanyi in cire yarinyar daga raina, as if samin ita akai a ciki."
Hassan kallansa yake, sai dai yasan mahaifinsa tabbas wannan kalaman daga zuciyarsa suke fitowa.
Kallansa yai yace " nafahimceka sai dai bansan meyasa zuciyata take blaming dinka ba, bawai baka iso kaso kowa bane sai dai Ummy doesn't deserve this treatment."
Abba cikin takaici yace " Ba so kadai bane a raina Hassan, mata nawa nake hulda dasu? Zance ba macen da ta taba burgeni ne? No kawai na riga nasa Ummynka ne beyond every woman, sai dai wannan karan it look like obsessed, inaji kamar dolene sai na sami yarinyarnan ko ta wani hali ne."
Hassan zaiyi magan, Ummy wacce hankalinta ya kasa kwanciya gani take kamar yanzun ma fada sukeyi yasa ta biyoshi, jin kalaman Abba ne yasa ta tsaya tana jinsu, sai dai yanzu kam idanunta ne suka zubo da kwalla, muryarta na rawa tace "it look like akwai babbar matsala a tare dakai"
A tare suka juya suka kalleta, Ummy ta karaso tace "just one month, ka bamu one month, ka daina kiranta sannan mu dukufa da addu'a musa nalamai ma su maka, in har a wata dayan nan dukda haka bakaji santa ya ragu a ranka ba ni na amince ka aureta."
Ummy!" Hassan ya fada yana kallanta, tai murmushi tace "in har a wata dayan kaima ka amince dani, karka nemeta sannan ko ta nemika ko a wayyane karka daga ko ka canza number"
Abba yace "na amince."
Hassann ya kallesu yana sanyin magana, Ummy tacee "Hassan please."
Idanunsa ya runtse, Abba yai murmushi tare da dafashi yace "Hassan bakasan dadin da nakeji ba, sauki ya fara samuwa da alama wannan auran rahama ne a gareka damu baki daya."
Hassan ya kalleshi sannan ya kalli Ummy, juyawa yai sannan yace "Shikenan Ummy tunda ke kikeso, sai dai ni ba one month ba ko shekara kikaba Abba bazan aminceba."
Ummy tai murmushi tace "nagode my eldest."
Juyawa yai yabar gun, mota ya shiga sannan ya fita daga gidan.
Jalila kam ta dade a zaune kafin ta dauko tiren abincin.
Akan dinning taga Sageer yana breakfast, da alama ma fitowarsa kenan dan tea yake hadawa.
Yana ganinta ya kura mata idanu har ta iso inda yake, gaisheshi tai, idanunsa na kanta yana nazarin fuskarta ya kasa amsa gaisuwar.
Kallansa ta sakeyi, yanzu kam ita kanta ta fahimci da abinda ke dakunsa dan duk fuskarsa ta canza, tace "Uncle bakada lafiya ne?"
Flask din ya ajiye sannan ya zauna yace "a'a me kika gani?"
Tace bakomai, wuceshi tai ta ajiye tiren abincin, kallanta yai yace " Yaya fa?”
Tace “ya fita.”
Shiru yai sai binta da kallo da yakeyi.
Jalila ta ajiye sannan ta fara dauraye kwanukan da sukai amfani dashi.
***********
Hassan na fita ya hau titi yana tafe yana tunani, meyasa yarinyarnan bata iya fita a ransa? Ya rasa me yasa in yaji ko yaganta cikin damuwa hankalinsa baya kwanciya.
Daren jiya ya tuno wajen karfe uku da rabi, kansa dake ta sarawa ya hanashi bacci, jin kamar ana kuka da magana, mikewa yai ya kunna fitilar gefen gado.
Jalila ce da alama mafarki take, kusa da ita yaje ya zauna yana kallanta, alamar kuka takeyi tana magana kasa kasa, kunensa yasa kusa da bakinta dake motsi.
“Dady, Mumy, Inna na kuyi hakuri karku kori Goggo dan Allah, na daina, na daina......”
Abinda take cewa kenan, hankalinsa da tausayinta sune suka kara ratsahi, addu’oi ya mata sannan ya kamo hannunta ya rike yana kallanta.
Ya rasa me yake tunani a sanda yake kallanta, meke faruwa dashi? Is he feeling guilty? Tunda yasan dalilinsa ne yasa aka mata auran dole? Sai dai abinda yakeji ya banbanta...... ya dade sosai har sai dayaji anata kiraye kirayen sallah sannan ya mike yai alwala.
A k