batasan hawaye na zubo mata ba tace "Hassan lafiya?"
Idanunya rufe kawai dan takaici, wato ita tana nan ta dauka mijinta na aiki ashe mata yake bi? Tun yaushe ya fara? Badai zina yake ba?
Sageer ya kalleta yace "Ummy akaishi daki."
Ta matsa tana share hawayenta, hannunsa ya zare daga jikin Sageer sannan yace "take care of Ummy zan karasa da kaina."
Sageer ya kalleshi har yai gaba, Jalila tabi bayansa da sauri.
Ummy kam jingina tai da motarsa tana share hawaye, Sageer yace "Ummy muje ciki."
Kallansa tai tace "Sageer kaji karar da ya saki? Bai tabayin irin haka ba, ina murna ya fara samun sauki, Sageer meke shirin faruwa?"
Sageer yai shiru tausayin Yaya da Ummy ya hanashi cewa komai, ta share hawayenta sannan tace " Sageer kaje gun Dr kajii ko da matsala."
Sageer yace "To Ummy, amma muje ciki ki zauna tukun na."
Hassan na shiga ya zauna a kasa jikin gado ya jinginar da kansa a jikin gado.
Jalila ta tsaya a bayansa ta rasa ta ina zata fara mai magana, ta dade a tsaye dan tayi wajen minti ashirin kafin ta juya jiki a sanyaye, hannu yasa ya riko hannu ya riko hannunta ta baya.
Juyowa tai da sauri tana kallansa, haka suka tsaya hannunsa na rike da nata ba kuma wanda yana wani magana, har na tsawon minti goma sha biyar, kafin ta tsugunna jin kafarta na dan zafi, ji tai ya saki hannunta.
Kallansa ta sakeyi sannan tace "Yaya jikin ne ko wani abun ne ya faru?"
Bai kalleta ba, sai dai yanzu ya mike daga kasan da yake ya zauna akan gado.
Sannan ya kalleta, idanunta na kansa ta kara cewa "yaya!"
Kallanta yai sannan yace " are u worried about me? Or are u scared?"
Ta kalleshi tace "Yaya dan Allah kadaina min tambayar nan, dan bansan me zance ba."
Yace "okay, jeki to."
Tace "naam?"
Yace "ba fita zakiyi ba na tsayar dake?"
Kallansa ta sakeyi tace " Yaya."
Kallan daya mata ne yasa ta mike tai waje jiki a sanyaye.
Zama tai a falon tana tunanin abinda ya faru yanzun nan, ya riketa sannan yace jeki, mekenan? Itakam tana kasa ganeshi wani sa'in.
**********
A Abuja kuwa Abba na gama waya ko kallan Hafiz baiyiba ya fada motarsa yai gaba hankali a tashe, kayansa kawai ya dauko a dakinsa sannan yai check out ya fito tare da ajiye motar.
Airport ya nufa dan hankalin sa a tashe yake, yana zuwa yai sa'a akwai jirgin da zai tashi karfe 3:00pm zama yai yana jira sai dai zuciyarsa ta kasa nutsuwa.
Lokaci nayi kuwa ya mike da sauri, ba nisa daga Abuja zuwa kano a jirgi kan kace me sai gasu sun sauka.
Bai tsaya neman Mamman ba kawai ya hau taxi zuwa gida.
Ummy na kwance a falo, tayi shiru tana tunanin Hassan, tana jiran dawowar Sageer daga gun Dr.
Jin an taba kofa ne yasa ta mike da sauri dan ta dauka Sageer ne.
Da sauri ta bude kofar tana cewa “Sageer me Dr din ya.......”
Ganin Abba yasa ta tsaya da maganar tana kallansa, kafin tace “ Sannu da zuwa.”
Kallanta yai jiki a sanyaye yace “Yauwa, sannan ya fara kokarin shiga ciki.”
Hannu tasa ta amshi jakarsa tai gaba fuskarta ba walwala.
Kallan falon yai sannan ya kalli hanyar sama, kafin yace “ina mutanen gidan?”
Tace “Ameera tace sai jibi zata dawo, Sageer ya fita.”
Yace “Jalila fa?”
Tace “Tana sama.”
Yace “Hassan fa? Ya jikin nashi?”
Kallansa tadanyi kamar zata fadamai sai tace “da sauki.” Sannan tai gaba.
Ba abinda yakesan ji ba kenan, so yake yaji ko wani abun ya faru dashi, sai dai baisan ta ina zai fara ba shiyasa yai shiru.
Ummy tana ajiye mai jaka ta juya zata fita, har takai kofa yai sauri yace “ kinje taron kuwa?”
Kallansa tai tace “banje ba.”
Yace “Naga kamar bakya farinciki da dawowata.”
Wani murmushin takaici tai kafin tace “banasan musu ko fada dakai daga dawowarka, mu bar maganarnan, kai wanka kafin ma shiryama abinci.”
Kallanta yai hartabar dakin, zama yai a bakin gadon sannan ya sa hannayensa ya rufe fuskarsa.
Jalila kam ganin hankalinta ya kasa kwanciya yasa ta mike ta kara turo dakin a hankali.
Yana zaune yasa farcensa yana karzar bayan hannunsa, idanunsa nakan bango yana tunani, idanunsa da fuskarsa a hade suke.
Jalila ta shigo ciki, har taje kusa dashi bai san tazo ba, hannunsa ta kalla taga yana ta karza har yaji ciwo ga jini nan.
Kallan tsoro tamai sannan tasa hannunta agun dayake karza, tana kallansa.
Dagowa yai ya kalleta sannan ya kalli Hannunta sannan ya kalli nasa hannun, sake kallanta yai sai dai yanzu idanunsa sun canza.
Idanunta ne suka ciciko tace “Yaya wani abun ne yafaru ko? Menene dan Allah? Ko akan abinda na fadama ne?”
Hannunsa ya janye sannan ya mike daga kan gadon zai nufi toilet.
Tace “kayi hakuri dan Allah, laifinane dana sani ban tsaya naji abinda suke cewa ba, sannan dana sani ban fadama abinda ke faruwa ba, kayi hakuri dan Allah, it’s all my fault.”
Tafada tare da share kwalla.
Juyowa yai ya kalleta kanta na kasa, tana share hawaye, ya dade yana kallanta kafin yace “ ba akanshi ba