anta ne ya shiga faduwa, tana kallansa.
Dayan hannun yasa ya juyo da fuskarta saitinsa yace “ tambayarki nake.”
Jalila idanuna suka firfito tace “ hmm.”
Saketa yai yana neman fita, da sauri tasha gabansa tace “Yaya Please!”
Kallanta yai yace “ in bakyasan in tambayeta ki fadamin meke faruwa?”
Jalila ta kalleshi tace “ wlh bansani ba nima, ranan nan ne na fita naji Abba nadan fada.”
Yace “yace me?”
Jalila tace “Yaya dan Allah.....”
Cikin zafi yace “ bani hanya”
Jikinta ne yai sanyi ta kalleshi sannan ta sanar dashi abinda ya faru, ta daura da cewa “Yaya dan Allah karka nuna ka sani, dan Allah.”
Gani tai a hankali idanunsa sun rikede, a hankali tadan matsa baya kadan, tana tsoron kar ya mazge ta.
Gani tai ya dau key din mota a zuciye yayi waje.
Biyoshi tai da sauri, sai taga ya fita waje.
Komawa tai kitchen gun Ummy tana cewa “Ummy yahkuri na dade.”
Ummy tai murmushi tace “bakomai, dama kinyi zamanki, Hassan ne ya fita?”
Tace Umm kawai dan batasan me zata ce ba daga nan......
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
" *Sending you smiles for every moment of your special day...Have a wonderful time and a very happy birthday!*" .......Phertyn Uwani😂 (El-Mustapha)
*37*
Haryasa key ya ta da motar sai ya kashe motar ya kwantar da kansa jikin kujera tare da rufe idanunsa.
Idanunsa ya bude wanda yanzu ya kara kadawa yai jaa sosai, wayarsa ya dauko ya kira number Abba.
Bayan sun gama yawo shi da ita yai parking din motarsa a gaban gidansu.
Zaliha ta kira number yayarta a waya tace "Aunty mun dawo."
Tace "to bari in fadamai ya fito."
Hafiz ta kalla wanda ke faman hada takardu tace mai "Taura yana waje."
Wasu takardun ya dauka ya fita, Taura na ganinshi ya kalleta yace "ki shiga ciki bari muyi magana."
Tace "a'a ku gama magana ni ina jiranka anan, banasan rabuwa dakai yanzu."
Taura yai murmushi sannan ya fita, tsayawa sukai da Hafiz suna tattauna wani abun.
Ringing din waya ne yasa ta kalli inda ya ajiye wayarsa, Eldest Son abinda taga an rubuta kenan.
Eldest? Tuno hoton maza biyun nan tai, ta tabbatar wanda ya maze din nan shine babban, murmushi naga tayi sliding ta daga wayar, a kunnenta ta kara.
Hassan shiru yai kafin can yace "Abba?"
Zaliha tadan sake murmushi tace "Bayanan."
Gani nai Hassan ya bude kofar motar ya fita yace "waye"
Gaban Zaliha ne ya fadi dan batasan ya akai ta tanka mai ba.
Cikin tsawa yace "waye nace?"
Bakinta ta shiga motsawa dan ta kasa magana, raban dataji tsawa ace ita akema har ta manta.
Hassan cikin tsawa da karfin gaske yace " kin fadamin ke wacece ko sai nazo nan na fasa miki baki."
Zaliha ta kalli inda Taura yake a rikice tace "Bari ba........"
Yace "ina mai wayar?"
Da sauri ta bude motar ta taho inda Taura yake jiki na rawa ta mika mai wayar.
Yana ganin sunan Hassan gabansa ya fadi, kallanta yai cikin takaici yace "Meyasa kika dagamin waya?"
Tace "bansani ba nima...."
Matsawa yai daga gun sannan ya kara wayar a kunnensa yace "Hassan!"
"Hassan? How can u call my name as if ba abinda ke faruwa"
Abba yace "Ya akai? Ina wani meeting ne Secretary gun ce ta dauka."
Hassan fuskarsa ta kara hadewa yace " Wacece wannan? Abba me kakeyi a garin Abuja? Ba dai......"
Kasa karasawa yai saboda kansa da yaji yamai nauyi, Abba a rikice yace "Hassan? Hassan jikin ne?"
Idanunsa ya runtse cikin takaici yace " Abba ko ka manta wacece Ummy a gareka? Ta yaya zaka yi mata haka?"
Abba a rikice yace "Hassan ba haka bane ka tsaya kaji."
Cikin takaici yace " Wallahi Wallahi Abba in dai ina numfashi a doron kasa bazan taba bari ka tozarta Ummy ba, sannan kayi gaggawar gayawa wannan yarinyar dan na tabbatar muryar yarinya naji, wallahi in har bata shiga hankalinta ba har cikin gidan ubanta zanzo in lahantata, in yaso a kamani."
Ya kashe wayar cikin takaici sannan ya saki wayar kasa cikin wani irin bakin ciki ya saki wani irin kara tare da tsugunnawa.
Jalila da Ummy dake kitchen suka fito da gudu saboda karar da sukaji, da sauri Ummy ta karasa kusa dashi tace "Hassan! Menene?"
Idanunsa na runtse bashi koma da alamar dagawa, Ummy ta kalli Jalila a rikice wacce itama gaba daya hankalinta ya tashi, tace "Jalila kira Sageer a daki."
Da gudu a juya, bata kwankwasa kofar ba saboda rikicewar da tai itama ta bude kofar.
Yana kwance daga shi sai singlet da gajerar wando, yana ganinta ya mike zaune da sauri, juyawa baya tai da sauri tace "Uncle kazo, yaya....."
Ai yanajin tace yaya ya sauko da sauri ya zari goduwar riga ta fito, shima ya fito bai ma karasa sa kaya ba sai a falon.
Yasan nanan a tsugunne duk yanda Ummy tai ta dagashi yaki, Sageer na zuwa ya dagashi da kyar, kallan Ummy Hassan yai idanun sa jawur kai kace garwashi.
Ummy