n kunna fanfo yanata zuba?”
Jalila ta kashe fanfon da sauri tana cewa “wlh ban kula ba sam.”
Ummy ta karaso ta dau cabbage ta fara yankawa tana cewa “ Hassan ne?”
Da sauri tace “ba shi bane.”
Tace “Nice?”
Jalila ta tsame hannunta tana cewa “ke kuma Ummy?”
Tace “eh mana, kinsan dan Adam ajizine, to ko Sagir ne?”
Tace “wlh ba kowa Ummy kawai abu nake tunani.”
Tai murmushi tace “ to ki rage yawan tunani haka, in kin kasa fahimtar abu ki tambayi wanda ya saki a duhu ko kuma ki nemi wanda zai fahimceki.”
Kai ta daga cikin jin dadi tace “nagode Ummy.”
Sannan ta ce “ina zuwa.”
Da gudu tabar kitchen din ta haw sama, tana hakki ta shiga cikinn dakin, yana kwance kamar me bacci ta shiga.
Kai ya girgiza kawai ba tare da ya kalleta ba, dan yasan in ba ita ba waye zai banko mai kofa haka?
Jalila ta isa kusa dashi tana hakki tace “Yaya!”
Idanunsa a rufe sai dai yadan yi motsi da hannunsa daya yake kan goshinsa, ta kara gyarawa sannan tace “Yaya dan Allah me kake nufi? Naga ni ba gida ba, ba yan uwa ba, in na dauketa in kaita ina?”
Ta karasa maganar tana hakki.
Bai bude idanunsa ba yace “ni zaki tambaya?”
Ta sa gwiwowinta a kasa sannan ta sunkuyo jikin gadon tace “ yaya tunda kai magana na tabbatar da abinda kake nufi,, shiyasa naketa tunani har Ummy ta bani amsa.”
Yanzu kam jin an anbaci Ummy yasa ya bude idanunsa ya dan kalleta, yace “tace me?”
“In tambayi wanda ya sani a duhu in har bangane ba.”
Ya gyara kwanciyarsa tare da juya mata baya yace “ ni ai banine na saki a duhun ba.”
Mikewa tai ta dawo ta bangaren daya juya tace “ Yaya kaine fa kace in dauketa kafin su dauketa.”
Yace “sosai haka nace.” Ya fada yana kallanta.
Tace “to ai shine ban gane ba.”
Yace “baki gane ba ko kwakwalwarki bata aiki yanda ya kamata?”
Baki tadan turo jin wannan bakar maganar, ya kalleta yace “na nawa kike ci a skul? Na tabbatar double number kike dauka.”
Fuskarta a dan hade tace “double din ai kala kala ne, ni na farko farko nake dauka.”
Yanzu ma bai san bakinsa ya dan murmusa ba, sai kallanta dayai yace “ what’s the difference?”
Tace “ mai daukan double number akwai yan 10’s akwai 20’s akwai 30’s har 50’s ma akwai kaga kuwa ba daya bane.”
Kai yadan jinjina kadan sannan ya sakala hannayensa tare da maida hankali kanta yace “ and?”
Tace “ mene?”
Yace “ u.”
Shiru tai tana dan kumburo baki sannan ta mike tace “Yaya ni danazo magana daban ka canza ta zuwa wani.”
Hannunsa yasa yadan bugi gefen sa wajen saitin cikinsa, kallansa tai sannan tace “in zauna?”
Da ido ya mata alamar eh, nan ta zauna tana kallanshi, ganin yanda ya kafeta da ido ne yasa tai saurin dauke nata idanun.
Hassan ya kalleta yace “ me yasa kika aureni? Bayan baki sanni ba?”
Dagowa tai ta kalleshi, yanayin idanunta suka canza, yace “am sry let me change the question, me yasa kika bari aka miki auren dole? Last time da na tambayeki baki bani amsar da ya dace ba.”
Jalila idanunta ne suka ciciko tana kallansa tana wani murmushin wanda kana gani kasan na damuwa ne ta dan rangwada kai gefe kadan tace “ ya zanyi? Bayan rayuwar mahaifiyata na hannunsu.”
Yace “ kin taba ganin rayuwar wani a hannun wani dan Adam irinsa?”
Bakinsa tasan rufe da labanta kafin ta kalleshi tanna share hawaye tace “she is too sick, wanda hakan ya tsoratani, sunce in ban aminceba bazasu taimaketa ba, how can i.......”
Hawaye ya cigaba da zubo mata, idanu ya zuba mata kafin yace “sai yaushe ne zaki gama?”
Ta kalleshi tana hawaye tace “mene?”
Da kai ya mata alama da fuskarta.
Ta share hawayenta tana cewa “ na gama.”
Gani tai ya mike ya zauna, sannan ya sa kafafunsa ta daya bangaren ya saukar kasa kamar mai shirin sauka sannan yace “ sai a fara canza mata asibiti, inda suma bazasu ganta ba kafin ta samu lafiya cikake.”
Da sauri ta kalleshi, tace “Yaya!”
Cikin wani yanayi ta kira sunan wanda kana ji kasan kira ne na jin dadi da ba zata.”
Mikewa yai tare da bude wardrobe, gaba daya ita kam ta kame a zaune tana mamakinsa, a yanda ta ganshi bata taba tunanin mutumin nan zai mata rana ba, ta dauka itace ake san ta taimakeshi batasan itace wacce za’a taimaka ba, sannan batasan zai ata rana a dan karamin zaman da sukai ba, sai gashi tana ganin side na halayensa kala kala, wanda ta tabbatar zaman taren da sukai, su kwana tare su tashi tare shine yasa ta fahimci hakan, lalai taga hallaci daga gunsa, da gun Ummy.
Batasan tayi nisa a tunani ba sai jitai yace “sai yaushe zaki fadama Ummy?”
Tace “ bansan in kara mata damuwa.......”
Da sauri tai shiru tare da juya kai, takowa yai a hankali zuwa inda take, yasa hannu ya juyo da fuskarta yace “Damuwarta?”
Yawo ta hadiya sannan ta mike da sauri ta matsa daga inda yake.
Hannu yasa a gefen cikinta ya jawota yana kallanta da idanunsa wanda suka canza.
Gab