ya kafeta da ido ne yasa tai saurin dauke nata idanun.
Hassan ya kalleta yace “ me yasa kika aureni? Bayan baki sanni ba?”
Dagowa tai ta kalleshi, yanayin idanunta suka canza, yace “am sry let me change the question, me yasa kika bari aka miki auren dole? Last time da na tambayeki baki bani amsar da ya dace ba.”
Jalila idanunta ne suka ciciko tana kallansa tana wani murmushin wanda kana gani kasan na damuwa ne ta dan rangwada kai gefe kadan tace “ ya zanyi? Bayan rayuwar mahaifiyata na hannunsu.”
Yace “ kin taba ganin rayuwar wani a hannun wani dan Adam irinsa?”
Bakinsa tasan rufe da labanta kafin ta kalleshi tanna share hawaye tace “she is too sick, wanda hakan ya tsoratani, sunce in ban aminceba bazasu taimaketa ba, how can i.......”
Hawaye ya cigaba da zubo mata, idanu ya zuba mata kafin yace “sai yaushe ne zaki gama?”
Ta kalleshi tana hawaye tace “mene?”
Da kai ya mata alama da fuskarta.
Ta share hawayenta tana cewa “ na gama.”
Gani tai ya mike ya zauna, sannan ya sa kafafunsa ta daya bangaren ya saukar kasa kamar mai shirin sauka sannan yace “ sai a fara canza mata asibiti, inda suma bazasu ganta ba kafin ta samu lafiya cikake.”
Da sauri ta kalleshi, tace “Yaya!”
Cikin wani yanayi ta kira sunan wanda kana ji kasan kira ne na jin dadi da ba zata.”
Mikewa yai tare da bude wardrobe, gaba daya ita kam ta kame a zaune tana mamakinsa, a yanda ta ganshi bata taba tunanin mutumin nan zai mata rana ba, ta dauka itace ake san ta taimakeshi batasan itace wacce za’a taimaka ba, sannan batasan zai ata rana a dan karamin zaman da sukai ba, sai gashi tana ganin side na halayensa kala kala, wanda ta tabbatar zaman taren da sukai, su kwana tare su tashi tare shine yasa ta fahimci hakan, lalai taga hallaci daga gunsa, da gun Ummy.
Batasan tayi nisa a tunani ba sai jitai yace “sai yaushe zaki fadama Ummy?”
Tace “ bansan in kara mata damuwa.......”
Da sauri tai shiru tare da juya kai, takowa yai a hankali zuwa inda take, yasa hannu ya juyo da fuskarta yace “Damuwarta?”
Yawo ta hadiya sannan ta mike da sauri ta matsa daga inda yake.
Hannu yasa a gefen cikinta ya jawota yana kallanta da idanunsa wanda suka canza.
Gabanta ne ya shiga faduwa, tana kallansa.
Dayan hannun yasa ya juyo da fuskarta saitinsa yace “ tambayarki nake.”
Jalila idanuna suka firfito tace “ hmm.”
Saketa yai yana neman fita, da sauri tasha gabansa tace “Yaya Please!”
Kallanta yai yace “ in bakyasan in tambayeta ki fadamin meke faruwa?”
Jalila ta kalleshi tace “ wlh bansani ba nima, ranan nan ne na fita naji Abba nadan fada.”
Yace “yace me?”
Jalila tace “Yaya dan Allah.....”
Cikin zafi yace “ bani hanya”
Jikinta ne yai sanyi ta kalleshi sannan ta sanar dashi abinda ya faru, ta daura da cewa “Yaya dan Allah karka nuna ka sani, dan Allah.”
Gani tai a hankali idanunsa sun rikede, a hankali tadan matsa baya kadan, tana tsoron kar ya mazge ta.
Gani tai ya dau key din mota a zuciye yayi waje.
Biyoshi tai da sauri, sai taga ya fita waje.
Komawa tai kitchen gun Ummy tana cewa “Ummy yahkuri na dade.”
Ummy tai murmushi tace “bakomai, dama kinyi zamanki, Hassan ne ya fita?”
Tace Umm kawai dan batasan me zata ce ba daga nan......
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*36*
Ameera ta kalli Aina’u tace “dan Allah kizo mu tafi tare.”
Aina’u ta maida kanta ta kwanta kan gado tace “dan Allah kimin uzuri, kema kinsan bazan iya zama a gidan ku kamar da ba.”
Ameera ta dan hade rai tace “kin san da haka me yasa ke da kike yar uwa har kika bari bare ta aureshi in har kinsan kina sanshi?”
Aina’u ta mike ta zauna akan gado tace “Ameera ni kike so in kai kaina gunsa?”
Tace “daga baya kenan, kema tun farko kinso rigima kinfi kowa sanin Halin Aunty Nana da yanda ta daura buri akanki, me zaisa ki wani fito da zancen wai kinasan yaya?”
Aina’u ta kafe ta da ido cikin rashin jin dadin kalamanta, Ameera ta mike tace “ in ba so kike zumuncinmu yai rauni ba ki cire wannan zancen, ki ajiye shi a cikin dakin nan, na rokeki da Allah.” Ta karasa maganar tare da shiga toilet.
Aina’u ta bita da kallo tasan gaskiya ta fada mata amma duk da haka sai dataji zafinta.
Komawa tai ta kwanta cikin takaici.
Ameera na fitowa ta kalleta sannan ta bude kofa ta fita falo ba tare da ta mata magana ba.
***********
Jalila tana zaune a falo tana kara tunanin kalaman Hassan, haka ta sauko tana girkin rana amma tana kara maimaita kalaman a ransa, me yake nufi? In ta dauketa ta kaita ina to?
Batama san Ummy ta shigo kitchen din ba sai ji tai ta tabata.
Kallanta tai da sauri tace “Ummy!”
Ummy tai murmushi tace “tunanin me kike haka? Ki