"
Ummy ta jinjina kai cikin jin dadi tace "na gani Jalila, ai tunda ya fita dake a mota nasan Hassan ya fara canzawa, ko Ameera bai taba fita da itaba a motarsa."
Jalila tai murmushin jin dadin yanda taga Ummy na farinciki.
Ummy ta kara rike hannunta tace "Jalila nagode sosai, nagode har bansan yanda zan miki godiya ba, nasan kina shan wahala da kuka da Hassan."
Jalila ta sunkuyar dakai tace "Ummy ki daina fadar haka dan Allah."
Ummy ta jawota ta rungume tace "Jalila mu dauki junan mu a matsayin uwa da yarta, mu ajiye surukantaka a gefe."
Ta dagota tana kallanta tace "Ameera bata fiya zama muyi hira ba, saboda makaranta in ta tafi tun safe sai uku da rabi sannan islamiya karfe hudu, tana dawowa assignment da gajiya su hanata zama ayi hira, Sageer kuwa shine ma muke hira dashi shikuma kinga namiji ne, balle kuma ince Hassan."
Tai ajiyar zuciya tace "inaso mu dauke junan mu da mahimmanci."
Jalila ta daga kai cikin jin dadi tace "To Ummy insha Allah."
Haka suka karasa dinning, Ummy ta bude kulolin sannan tai murmushi tace "inama Hassan zai sauko muci abinci dukan mu?"
Jalila ta kalleta, Ummy tace "later, mu bi abin a sannu, kar san zuciyata yasa mu rikita komai."
Jalila ta daga kai tare da cewa to Ummy.
Ummy tace kizo ki kaimuku naku, Jalila tace "ke fa? Ke kadai zaki yi breakfast?"
Tace "Sagir na nan nasan ya kusa fitowa."
Jalila ta zo ta zuba musu ta hau sama dashi.
Tana tura kofar yana kokarin saukowa daga kan gado da alama tashinsa kenan, Jalila ta ajiye tiren sannan tace "Yaya ka tashi? Ya jikin?"
Kallanta yai sannan yace "Ummy fa?"
Ta dago tana cewa tana falo, ya mike ya nufi toilet.
Tana gyara gado ya fito, dayan bangaren ya karasa yana tayata gyarawa, kallansa tai tace "yaya barshi, ka zuba abinci."
Bai tanka mata ba har ya gama sannan ya zauna ya mike kafa yace "zo ki zubamin, tunda kin damu sai naci yanzu."
Jalila tana murmushi ta matso ganin zata wuce yasa ya shiga kokarin janye kafarsa daya mike, ita kuma da sauri ta taho yana kokarin janye kafar ita kuma bata kula ba tai tuntube, tahowa tai zata fadi ta gaba, da sauri yasa hannu dan tareta, duk da haka sai da shima ya kai kasa, ta fada kansa kif.
Hannunta na hagu ya bugi bango, da dan sauri tai kara, da sauri ya kalleta yace "Jalila? Menene?"
Kallansa tai tace " bigewa nai."
Harararta yai yace " raguwa, shine harda wani kara haka? Ni da kika danneni fa?"
Ta dan dago ta kalleshi, yace "sai yaushe za'a dagani?"
Da sauri ta murgina gefe sannan tadan hade rai kadan, ya kalleta yace " karki ma fara shirin yin pretending I won't fall for it twice, ki zubamin inci ko ki dauke abincinki."
Jalila bata san sanda tai dariya ba tace "au in ban zuba ba sai kaki ci?"
Yace "Ehem, kina wasa ne?"
Tace "a'a ina na isa in hana dan Ummy abinci?"
Ta fada tana zubamai a plate, kallanta yai bayan ta gama zubawa sannan ya fara ci.
Itama ta xuba taja gefe tana ci, batai auni ba taji yace " yaushe zaki koma?"
Kallansa tai tace "Ina.....?"
Sannan ta kara fadada dariyarta tace " Gun Goggo?"
Bai kalleta ba, da sauri ta tsame hannunta ta matso inda yake tace "Yaya da gaske?"
Kallanta yai sannan yace "me kike shirin yi? Yanzun ma pretending din faduwa zakiyi dan in tare ki?"
Kallansa tai tana dariya sannan ta matsa daga matsowar da tai tana cewa "wlh dazu faduwa nazo yi."
Bai kalleta ba, ta jawo kwananta kusa kadan tana cewa "Yaya yaushe zamu? Yau? Gobe?"
Tea yadan kurba sannan yace " yanda kika damu da Mahaifiyarki me yasa kike tsoro?"
Har tayi shiru kamar bazata amsa ba kafin tace "a haka na taso, daga ni har Goggo bamu da daraja bare matsayi."
Idanunsa na kanta yana dan nazari kafin yace "ki binciki mahaifinki, banaji akwai igiyar auranta akanshi."
Jalila ta kalleshi tace " To yaya, ni tsoro nake karma su kara dauke Goggon."
Kamar bazai tanka mata ba sai taji yace "sai ke ki dauketa kafinsu su dauke ta."
Da sauri ta kalleshi tace "kamar ya?"
Abincinsa ya cigaba da ci, yana gamawa ya mike yai toilet, shiru tai tana nazari kalamansa wanda bata fahimta ba sam.........
*******
Inna ce ta kalli Mumy tace " waccen sokon yaje gun Jalilan?"
Mumy tace "Inna wai dan Allah meyasa kike haka ne? Karfa ki manta mahaifin jikokinki ne."
Tai dan tsaki tace "ni tambayarki nake yaje ko baije ba?"
Tace "wai tayaya zaije gidan sirikansa yana namiji?"
Inna tace " ta yaya zaije? Ki tashi ki sanar dashi in har shi ya kasa zuwa ya ja mata kunna ni zan yi abinda ya dace, tun kafin zance yakai gun matar Taura har yaje gunta"
Mumy tace to ta mike ta sauko fuskarta a hade.
*******
Zaliha zaune a cikin mota tana jiran Abba wanda ya fita siyo musu abu ya dawo, ta sa hannu ta dau wayarsa, ba security hakan yasa kawai ta bude ta shiga gallery tana kallan hotuna, ba wasu pictures bane a ciki yawanci na aikinsa ne, sai Matarsa da ta gani wace ta riga dama ta santa, sai Ameera data gani daga baya wace taga tsantsar kamar matarsa a