NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 66 of 172

n ya juya ya fita, Ummy ta kallesu cikin farinciki sannan ta kalli gefen gado, Abinci Jalila ta ajiye mata da ruwa da paracetamol wanda ta tabbatar a cikin magungunanta ta dauko mata. Murmushi tai sannan ta hadiye maganin kawai ta kishingida. Hassan haka ya hau da ita steps din har yaje kofarsu, kallanta yai yaga tana kif kif da ido, hannu yasa ya bude kofar sannan ya shiga ciki. Gani nai yayi hanyar toilet da ita ya bude kofar, yana neman shiga, Jalila kam jin ya sake bude kofa yasa ta bude ido ta kalleshi. Ganinshi tai yana neman shiga toilet da ita, da sauri tace "Yaya ina zaka kaini?" Yace "au kin tashi?" Tace "ina zaka kaini?" Yace "kamar Ummy cewa tai in kaiki bandaki in taimaka miki kiyi wanka." Da sauri ta fara kokarin kwace kanta tana cewa "wlh banji tace haka ba. Sauke ta yai a ciki sannan yace " me tace to?" Yafada tare da tare hanyar toilet din. Jalila ta kalleshi tace " cewa tai sai da safenku." Hassan yace "hmmm bakiji farkon ba kenan, ni kuma na ji." Kallansa tai batace komai ba, fitowa yai yasa hannu yana neman rufe kofar. Da sauri ta rike tana cewa "yaya menai? Naga lafiya muka dawo." Yace " idanki biyu kikasa ma daukeki?" Tace " ba idona biyu ba Allah daga baya na farka." Yace " da kika farka fa?" Tace "yahkuri wlh ni kunya naji." Kallanta ya tsaya yanayi. Kanta ta maida kasa tana kara rike kofar, can ta saki dan kara ta rike hannunta tace "wayyo hanuna." Kallanta yai yace "hannu?" Jinginna tai da bango tana dan murza hannun, sakin kofar yai ya shigo yana cewa "menene?" Da sauri tai waje da gudu tana dariya. Tsayawa yai kawai yana kallan ta, lalai yarinyar nan. Dariya ta shiga yi tana cewa "yaya wai harka shiga?" Hassan ya hade rai ya fara nufo ta, ganin yanda idanunsa suka canza yasa ta tsaya cikin tsoro tanayin baya. Sai dayaje daf da ita sannan ya zauna akan gado bai ce mata komai ba ya dau littafinsa. Kallansa tai jiki a sanyaye tace " Yaya bakai dinner ba." Kallanta yai yanzu ma baice komai ba, tai shiru ta zauna a gefen gado daga karshe. Shiru ne ya ratsa dakin kafin can yace "Jalilah!" Kallansa tai da sauri, yauce rana ta farko da ya kirata da sunanta cikin wannan muryar, murya ba mai dauke da zafi ko fada ba. Idanunta na kansa yace " Jalilah Please take care of Ummy." Idanunta na kansa tana kallansa ta daga mai kai alamar fahimta sannan tace " Insha Allah." Haryanzu idanunsa na kanta yace " Nagode." Kanta ta sunkuyar sannan tace "nima na gode Yaya da taimakon da kamin." Yace " me kika ce ma Goggon taki?" Ta kalleshi da raunanan ido tace " ban iya cemata komai ba, bansan ta ina zan bulo ba, bansan me zan ce mata ba." Ta karasa magana tana share kwalla, kallanta yai yanasan lalashinta sai dai bai san ta ina zai fara bama. Kansa ya dauke daga gunta, wayarsa ya dauka ya dubo sunan Abba. Rabon daya kirashi harya manta, sai dai shi Abban ya nemi shi. Dialing yai yana kallan agoggo, goma saura. Yanajin wayar har ta gama ringing bai dauka ba, idanunsa ne suka kara canzawa ya sake kira, tana daf da katsewa Abba ya daga cikin mamaki da shakka. Kallan Abokinsa yai sannan ya mike daga falon ya fito waje. Ya daga yana cewa "Hassan!" "Abba kana ina?" Jalila ce ta kalleshi da sauri, Abba yace "nayi tafiya ne, baka tambayi Ummynka ba?" Hassan yace " na dauka akan tafiyarne kukai fada?" Abba cikin mamaki yace "Haka tacem?" Yana mamakin kiran da Hassan yamai da kuma mamakin yanda yake tambayarsa, duk da Hassan na tsananin san Ummy bai taba shiga maganarsu ba, me ke faruwa?" Hassan harzai sake magana sai kuma ya kashe ya cillar dawayar gefen gadon. Jalila tai shiru tana kallansa, mikewa tai tai shimfida dan yanda ta ganshi tasan da matsala. Bata dade da kwanciya ba bacci yai gaba da ita. Hassan kam ya dade kafin ya mike ya sauko kasa. Sai daya leka Ummy yaga tana bacci sannan ya juya ya koma sama. Jalila ya kalla wacce ke bacci, daga gefen gado ya kwanta har bacci ya daukeshi. Yanda jikinsa ke kadawa da yanda yake abu kamar maiyin kuka yasa cikin baccinta ta farka. Da sauri ta kunna wayarta sannan ta kunna fitilar dakin. Bakinsa sai kakkarwa yakeyi, da sauri ta karasa kusa dashi ta kamo hannunsa. Ganin yana neman fadowa daga kan gadon yasa ta rungumeshi tana hawaye tana kiran sunansa. Idanunta a runtse, hawaye kawai ke zuba. Ta kankameshi, sun dade a haka kafin nimfashinsa ya fara daidaituwa. A hankali ya bude idanunsa ya zubasu akanta, hawaye kawai take tana kiransa. Yanda ta rungumeshi ne yasa ya kara kallanta sannan yace "Jalila!" Idanunta ta bude ta kalleshi, bakinta na rawa tace "Yaya?" Yace "wannan rikon fa?" Sakeshi tai tana kallansa, ya kalleta yace "baki iya addu'a bane sai kuka da kiran sunana?" A hankali tace "banyi islamiya ba." Kallan mamaki ya mata da tausayawa, sannan yace " kukan fa? Are u worried about me? Or are u scared?" Kallansa tai bata iya cewa komai ba.
🏠