da ita tace “dama
Bakiyi bincike ba?”
Inna tai shiru kafin tace “ muna cikin tashin hankali, idanun yaran nan ba tsoro ko fargaba a ciki sannan da alama baya ragama wanda ya tabashi, me kuke tunanin zai faru in yasan abinda akama matarsa? Sannan canjen da mukai muka bashi Jalila a maimakon Safeena?”
Mumy ta kalli Dady tace “Dadyn Yasmeen!”
Dady ya kalli Inna wacce ke kallansa yace “ hakan bazai faru ba, ni da kaina zan sanar da ita karta kuskura ta sanar dashi komai, kuskuren sanar dashi Mahaifiyarta datai ya isa.”
Inna ta jinjina kai tace “u have to take care of her, in ba haka ba ni zan bulo mata ta bayan gida, zan sata dana sanin da bata gaba yi ba daga ita har uwarta.”
Dady yace “insha Allahu baza’a sake ba.”
Mikewa tai ta hau sama.
Tana tafiya ya mike a zuciyd ya shiga dakinsu.
Mumy ta bishi da sauri tare da rungumeshi ta baya tace “Darling.”
Hannunsa ya zare yace “meye hakan? Kina abu kamar yarinya?”
Ta kara kankameshi tace “Dadyn Yasmeen am sry.......”
Kallanta yai kamar zaiyi fada, da sauri ta sumbaceshi...........
*************
Ummy ce ta kalleshi tace “ ina zakaje da har kake san in wakilceka akan taron da yake da mahimmanci?”
Yace “Abuja zan koma dan akwai abu mai mahimmanci da nake sanyi.”
Ummy ta kalleshi tace “yafi wannan mahimmanci?”
Abba yai shiru yana duba abu a computer sa.
Ummy tace “ ni na kasa gane abinda bazaka iya fadamin ba”
Cikin zafin rai yace “wai meke damunki ne? Dolene ko wani abu na rayuwarta sai na sanar miki?”
Da karfi ya budo kofar wanda ya sa suka kalli kofar a tare, kallan Abba ya shiga yi idanunsa sun canza sosai.
Yanda yake kallan Abban ne yasa Ummy ta matso da sauri ta sa hannu ta riko hannunsa tace “Hassan meye hakan? Taya zaka banko kofa haka bako sallama?”
Idanunsa na kan Abba haryanzu wanda gaba daya Abba ya gama shan jinin jikinsa.
Hassan ya daure yace “mekenan?”
Ummy tace “ mekenan kamar ya?”
Hassan bai kalli Ummy ba idanunsa nakan Abba yace “me Ummy tai da har kake mata fada haka?”
Ummy tasa hannu da karfi ta turashi waje sannan ta fito itama, ta rufo kofar sannan ta kalleshi tace “muje.”
Ta fada tana jan hannunsa, dakyar ya hau saman sannan ya kalleta cikin takaici yace “Ummy me kika mai yake fada haka?”
Tace “ ba abinda yamin nice namai lefi shiyasa yakemin fada akan abinda nai.”
Kallan ta yai dan shikam bai yarda ba, to ko laifin ma tamai taya zai hauta da fada haka? Ummy ta kalleshi tace “Ina Jalilan?”
Yace “Ummy kin tabbatar ba abinda ya miki?”
Tace “sau nawa kake so na fada ne? Ina tambayarka Jalila, badai ajiye ta kai a hanya ba?”
Yace “Tana nan, kawai ya wuce dakinsa.”
Zama yai a bakin gado yana tunani, dolene ko wani abu na rayuwata sai na sanar miki?
Kallaman Abba ne ya sake dawo mai, meke faruwa?
Ummy tana sauka ta koma dakin, Abba ya kalleta yace “me kika cemai? Tace “ kome nacemai bana tunanin nima ya zama dole in sanar dakai.”
Abba ya matso kusa da ita yace “Ciwon sa fa? Ya tashi?”
Ummy ta kalleshi tace “ kaje ka duba.”
Ta matsa daga kusa dashi.
Abba yai shiru yana tunani sannan ya koma ya zauna agefen gado.
***********
Bayan magrib yana zaune yana karatu, naga ya rufe littafin ya sauko zuwa mota.
Kallo daya zakamai ka fahimci yana cikin bacin rai tsantsa.
A asibitin yai parking sannan ya fito, duk yanda yaso ya duba Nurse din a reception din bai ganta ba.
Kawai komawa yai mota ya zauna, ya kwantar da kansa akan kujera.
Jalila kam sunata hira da Goggo taga isha’i tayi.
Wayarta ta dauko tana dubawa ko zai kirata, ta ina zai kirata? Bayan bashi da numberta? Itama haka.
Ajiyar zuciya tai sannan ta ajiye wayar.
Goggo ta dau wayar tana kara kallo tace “gaskiya wayar nan tayi kyau ta birgeni, mahaifiyar Sagir ce?”
Tace “Hmm.”
Goggo tai murmushi tace “ karki damu ina warkewa zansa ya turo ai auran.”
Wani film akeyi a tv dake dakin, saurayin ta na waje yana ta jiranta ita kuma bata sani ba tana cikin gida suna ta hirar su
Mikewa tai ta dau hijab dinta tace “Goggo ina zuwa.”
Ta fito, tana tafe tana cewa kai inaa.... ta ya zai zauna jirana? Au ko bai san inda nake ba na tabbatar zai sa a nemi ni.
Tana fitowa kawai ta hango motarsa, mamakinne ya kamata ta karaso gun motar a ranta tana cewa “ kai.... ba shi bane, kanta tasa tana leka motar.”
Hassan na kwance ya bude idanunsa, gani yai ana leko cikin motar, tunda akwai haske fitulun waje.
Hassan ya zuge glass din motar yace “ meye hakan?”
Tace “kai!!!! Kaine da gaske, me kake anan?”
Yace “ me nake kuwa, bakisan wannan shine hubby dina ba?”
Tace “zama a mota?”
Bai tanka mata ba yace “ muje?”
Tace “bari nama Goggo salama, Yaya bazaka shiga ba?”
Kansa ya kawar gefe.
Ta fita ta ma su Goggon salama, goggo ta bita da kallo tana tunanin tabbas akwai