i?"
Kallanta yai sannan ya juya kansa, shiru tai kafin tace " Bansan me zanyi ba."
Yama rasa mai zaice hakan yasa ya sa hannu zai dauki littafinsa, da sauri ta rike littafin.
Kallanta yai tace "Please!"
Yauce rana ta farko a rayuwarta da take roko da neman taimako akan 'yancinsu, aduk lokacin da aka musu abu a da sam bata kawo komai sai takaicin yanda ake wulakantasu, amma bata taba tunanin zata kwaci kanta ba, itadai kullum fatanta tai aure ta dauke Goggonta.
Hassan yace " in bakida abin cewa ki bari sai kin samu sai kimin magana, bance zan taimaka miki ba bare kisa ran zanyi, na dai ce ki fadamin ne kawai inji ko zan iya, i hate meddling in someone's life."
Bata saki littafin ba tace " Ban taba tunanin nima har akwai lokacin da zan nemi taimakonka ba, ganin halayenka, sai dai kai kadai ne a duniya a yanzu da zaka iya taimako na, Yaya dan Allah."
Yace " bai dameni ba, Ita mamar taki haryanzu suna tare da wanda ya haifeki ne?"
A ranta tace "ina laifin kace mamanki da babanki?"
Amma a fili tace "eh sai dai bansan wani irin zama ake ba wanda maganar mutunci bata hadasu."
Littafinsa ya kwace yace " to meye matsalar?"
Tace "naam?"
Yace menene matsalar ta koma gidansu mana."
Jalila ta kalleshi jiki a sanyaye, kallanta kawai yai wanda hakan ya nunamai can din ma dai ba magana.
Ya dade baice komai ba wanda har jikinta yai sanyi kafin taji yace "ki shirya gobe muje ki dubata."
Da sauri ta kalleshi sam hankalinsa baya kanta ya maidashi kan littafi, kamar bashi yai maganar ba,
Tace "Bansan asibitin da suka canza mata ba."
Bai tanka mata ba, tace "Yaya in mun dubata sai me zamuyi?"
Yace "later."
Tana shirin magana ma sai taga ya mike ya wuce toilet, ajiyar zuciya tai tace "kai wannan matarka ta shiga uku."
Sai tai shiru tace au ahh ashe fa nice ko?
(Nace kila nice.......lol)
Mikewa tai ta fito tana cewa "da alama bai fahimci ina na nufa ba, ni ba dubata nakeso ba, darajarta nakeso su sani balle har su kara tunanin rainata."
Haka ta fito ta sauka kasa, tana san yima Ummy saida safe.
Tasa hannu zata bude kofar taji muryar Ummy tace " wai meke damunka ne? Bansan me yasameka ba yanzu komai sai ka fara neman yin fada, scammers ka hadu dasu ne ko me?"
Yace " ke ce yanzu bansan meke damunki ba, bansan yaushe kika fara takura haka ba, dolene sai naci abincin......?
Jalila ta juya da sauri a ranta tana cewa " mekenan?"
Komawa tai sama da sauri, bayan sunyi sallah sannan taga yadanci abinci kadan, a ranta tace "in mace tayi ba wani abu amma namiji?"
Hassan ya hau kan gado ya zauna ya dau jornal dinsa, a ranta tace "wai baya gajiya? Daga zama da karatu sai fita?"
Wayarta ta dauka tana dan lalatsawa, lalai ta kosa gobe tayi ta nunama Goggo wayarta, amma zasu ganta kuwa? Bayan basusan sunan asibitin ba? Kallansa tai tanasan kara mai magana amma ta kasa.
Meya faru tsakanin Ummy da Abba? Ta fada mai? Can tace "hmm wannan mutumin? Salan yace gulma naje yi?"
Kafa yasa ya tura bargon dake kan gadon zuwa kasa.
Jalila ta kalleshi, ganin ba alamar shi yayi yasa ta dauko bargon ta na neman maidawa kan gadon, yace "in kinaso kiyi amfani dashi."
Da sauri ta kalleshi tace "dagaske?"
Bai tanka kata ba, ta dauka tana murmushi ta shimfida, ta hau ta luluba da bedsheet ga pillow yaukam kwanciyar ta mata dadi, wayarta ta dauko tana kara latsawa.
Haka tai ta latsa wayarta har tai bacci.
Juyowa yai ya kalleta, gani nai ya kura mata ido daga inda yake, kamar yana nazari akan wani abu.
Can sai naga ya gyara ya kwanta, bai dade ba bacci yai gaba dashi.
Washegari ma Alhamdulila anyi sa'a abin nasa bai tashi ba, bayan yayi alwala yasa kafa ya dan buge ta dan dama haka yake tashinta.
Idanu ta bude ta kalleshi, kallanta yai sannan ya mata alama data mike, Jalila ta tashi ta dauke da bargon daga gun, ga fili nan a dakin amma shidai anan yake sallah.
Toilet ta shiga shi kuma ya tada sallah.
Sai wajen karfe 7 ta tashi ta kasa ma baccin saboda ta matsu ya tashi su tafi gun Goggo, saukowa kasa tai dan fara aikin abinci saboda yana tashi itakuma ta gama komai sai tafiya.
Ganin dakin Ameera tai a bude, a ranta tace "ta dawo ne?"
Dakin ta nufa ta kara tura kofar, me zata gani?
Ummy ta gani a kwance tana barci.
Meke faruwa?
Badai fadan da sukai jiya bane haryakaisu ga haka?
Gyara kofar tai ta juya a hankali tabar gun ta nufi kitchen.
Aikin breakfast take amma sam hankalinta nakan Ummy, ta rasa meyasa batasan wani abun ya bata mata rai sam.
Tana aiki har masu aikin gidan suka zo, suna fara kwankwasawa ta fita da sauri ta bude musu kofar, bataso a tashi Ummy.
Gaisheta sukai sannan suka fara aikin shara da gyare gyare, saboda girman kasan.
Sagir ne ya fito ya hangota a kitchen tana ta aiki, tsayawa yai yana kallanta inama matarsa ce? Da yanzu zuwa zaiyi kawai ta bayanta ya rungumeta.
Da sauri ya fara a'uziyya saboda neman tsari daga shaidan, komawa ciki yai da sauri ya zauna a gefen gado sannan ya k