NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 58 of 172

saboda tsoro. Yau abin yafi na jiya shiyasa hankalinta ya tashi gashi su biyu a daki, kuka kawai take tana jinigashi. Sai dan karatun data iya datake yi, idanunta ta rufe kawai dan batasan ganinsa a haka gaba daya ya canz kamar mahaukaci ko mai farfadiya ko mai aljanu. Kuka take tana kiransa wani sain tai karatun idanunta gam, har batasan abin ya lafa ya bude idanunsa ba. Addu'oi yai sannan ya kalleta, tausayinta ne ya kamashi, yarinya karama a maidata mai jinya? Hannunta da take tabashi dan ya tashi ya rike. Idanunta ta bude a hankali a tsorace, ta kalleshi. Yace "kukan meye hakan?" Bakinta na rawa tace "Yaya?" Yace "mutuwa akai?" Kai ta girgiza, yace "to meye hakan?" Tana kuka tace "bakomai." Yace " meyasa baki nemi sanin wanda za'a baki ba?" Tace "kamar ya?" Yace "bakida 'yanci ne? Ko tsabar biyayya ce tasa? Ni naji inada lalura wanda ban isa in zabi matar da nake so ba, kefa?" Tace "nima." Nima? Ta share hawayenta da dayan hannu "ni Goggo batamasan nayi aure ba." Abinda ta fada kenan a ranta batasan a fili tai ba sai jitai yace " Goggo?" Kallansa tai sannan ta kakaro murmushi tace " hannuna." Sakar mata hannu yai sannan ya mike zaune yana kallan agoggo, mikewa yai ya nufi toilet ba tare da ya sake kallanta ba. Kallansa tai a ranta tace " ikon Allah, wato wani sa'in sai kaga Allah ya baka komai sai ya hanaka wani abun, kalli yanda ake sanshi a gidan nan, batasan ba kodan bashi da lafiya ne amma kaf gidan nan yanda suke mai sai kasan sanda sukemai daban ne, wanda ko kwana daya ko wuni mutum yai dasu zai fahimci hakan. Mikewa tai bayan ya fito tai alwala, kafin ta fito ya tada sallar ta fita falo tai sallarta sannan ta kwanta akan kujera, yau kam baccin bai dauketa da wuri ba tayi luff akan kujera tana jin kira'ar qur'ani mai dadin gaske wanda ta tabbatar radio ne yake aiki, tanasan taga tana karatun qur'ani ko ba kamar haka ba amma dai taga ta iyashi, in sultan na karatu a gida ji take inama itace. A haka har bacci yai gaba da ita. Hassan kam ya dade akan sallaya kafin ya kwanta. *********** _Bayan kwana hudu._ Goggo ce ta kalli lantana tace "Lantana Jalila bataso ba da ina barci? Lantana tace "eh." Goggo tai shiru "yau kwanana hudu kenan a sabon asibitin nan amma banga Jalila ba wanda na tabbata indai har da lafiyarta bazata taba iya kwanakin nan haka batazo ba, sannan ba wanda take gani abinci kawai suke aiko mata, bayan sanda zasu canza mata asibiti sai da suka sanar da ita Jalila nacan ma tana jiranta. Meke faruwa? Anya ba wani abun sukama Jalilanta ba kuwa? Wannan tunanin ne yasa hankalinta ya tashi, har jininta ya sake hawa, matar da ake tunanin sallamarta nanda kwana biyu. Goggo kira kawai take a kira mata Jalila. ******* Itakam Jalila kalaman Hassan sune sukai ta mata yawo. Gashi hankalinta ya kasa nutsuwa saboda rashin Goggonta, duk da yanda Ummy ke iya kokarinta na ganin Jalila ta saki jiki da gidan. Sagir kam baifiya ma zama ba saboda hankalinsa tashi yake inyaga Jalila. A hankali ta turo kofar, yana kwance a kan gado yana karatu, ta rasa mai yasa ita ko irin wayarnan taga yanayi ko yana dannata bayayi. Shiga cikin dakin tai ta tsaya tana dan wasa da hannunta. Bai kalleta ba bakuma tasa ran zai kalleta din, hakan yasa ta matso kusa dashi kadan. Nan ma bai kalleta ba, daurewa tai tace "Umm Yaya!" Bai kalleta ba yace "menene?" Tana wasa da hannunta ta rasa mai zatace, ganin batada niyyar magana yasa ya cigaba da abinda yakeyi. Jalila kam ganin tsayuwar bamai karewa bace gashi ita tasan zata iya fadama Sagir sai dai ta ina zata fara kebewa dashi ta sanar mai? Sannan mai zaiyi tunani? Gwara dai Hassan din tunda koma menene at least yasan wani abin na daga rayuwarta. Ganin haka ma sai ya mike yadau waya da key din motarsa yana neman fita. Cikin hanzari ta riko gefen rigarsa, tsayawa yai sannan ya juyo ya kalleta sannan ya kalli rigar tasa inda ta rike. Tace "Hmm Yaya magana zamuyi." Da kai ya mata alama da yanaji, ta sakeshi sannan ta tsaya. Yace " in baka san me zakice ba ni zanyi gaba." Jalila tana gani ya juya ta kara riko rigarsa da sauri, kallanta ya juyo yai sai dai yanzu yanayinsa yadan canza yace " meke nan?" Tace "Yaya!" Matsowa ya fara yi tana matsawa baya, tsoro ya fara ratsa mata har sai da sukaje jikin gado ta fada kan gadon, gani tai ya rufo kanta, tsoro da fargaba suka kamata, idanunta suka firfito ganin namiji akanta haka. Idanunta ta runtse gam cikin tsoro, can taji shiru, a hankali ta bude idanunta a tsaye ta ganshi yace "2minute na baki." Tace "Yaya......" Yace "will you stop calling me?" Magana nace kiyi ba kirana ba. Ta daure tace "Yaya bansan ya zanyi ba." Ya kalleta alamar me take nufi. Tace "maganar Goggo." Yace "to menene nawa a ciki?" Tace "naam?" Yace "menene nawa a ciki da kike fadamin?" Shiru tai dan batasan me zata ce ba, agoggon hannunsa ya kalla yace "minutes din da na baki sun cika." Ya juya ya fit
🏠