a sannan ta koma ciki, gaba daya itakam abin duniya ya dameta, Ameera ta ajiye tiren sannan ta kalleta tace “ga na yaya nan sai kici anan, shi nasan ba yanzu zai dawo ba.”
Ajiye abincin tai ta fita.
Jalila kam a zaune kawai take akan gado tama rasa ta ina zata fara tunanin abinda ke faruwa.
Ganin ta rasa amsa kawai ta dauko hijab dinta ta sauko, su Ummy na cin abinci ta sauko kasa, kusa da Ummy taje ta gaisheta sannan ta gaida Sagir, Ummy tace “zauna muci abinci.”
Jalila wacce ta fito dan sanar da ita tana san zuwa gun Goggo tai shiru tana wasa a hannunta.
Ummy ta kalleta tace “Ya akai Jalila? Wani abin kikesan fadamin?”
Dagowa tai ta kalli Uncle sannan ta kalli Ummy.
Sagir ya kalli Ummy yace “ko jikin ne?
Ummy ta kalleta tace “Jikin ne?”
Jalila da sauri tace “bashi bane.”
Ummy tace “to menene?”
Jalila ta kalleta sannan ta sake yin shiru, Sagir ya yace “ asibitin zaki koma?”
Kallansa tai sannan ta kalli Ummy, Ummy tace “wai haka?”
Jalila ta daga kai, Ummy tai murmushi tace “menene to da kika kasa fada? Ki zauna kici abinci sai kuje da Sagir.”
Kallan Sagir tai da sauri, sai dai batace komai ba.
Ummy tace “in bakya san ci anan ki hau sama kici kafin ya gama.”
Jalila tace “nagode Ummy.” Sannan tajuya tai ta hau sama.
Zama tai a falon tai shiru Hassan take hangowa abinda yai dazu.
Kanta ta kwantar akan kujera, Muryar Ameera taji tana kiranta, nan ta mike ta sauko ko dakin bata koma ba.
Da zata fita Ummy ta kirata, Jalila ta juya taje gunta, Ummy ta miko mata leda sannan tace ki gaisheta, dan gwarama da kika tuna min yau kije, dan Abban Ameera inya dawo ba lalai ya barki ki fita ba, bayasan fita.”
Jalila ta amshi ledar tana godiya.
A bakin mota ta hangoshi a tsaye, nan ta karasa kusa dashi, gani tai ya bude mata bayan motar sannan ya juya ya shiga gun zaman driver tare da kunna motar.
Rufe kofar motar tai yaja suka fara tafiya, Motar tayi shiru sai karar redio dake tashi a cikin motar.
Sunyi tafiya mai dan tsayi kafin can yace “Jalila.”
Idanunta na jikin window tace “naam.”
Yace “Jalila nasan na miki laifi sai dai nan gaba zaki fahimci dalili na nayin hakka sannan na tabbatar a lokacin zaki san abinda nake nufi da kalamai na.”
Kallansa tai sannan ta daure tace “ magana ta wuce, sai dai meke damun Yayan naka?”
Shiru yai kafin yace “Ni kaina ban sani ba, dukanmu yan gidan ba wanda yasan meke damunshi, shikadai yasan abinda ya faru a lokacin.”
Lokacin?
Yace “ eh lokacin da su Husain da Nazir dan kanin Abba.”
Jalila tai shiru batace komai ba, Sagir ya kalleta ta madubin gaban motar, yana tsananin san yarinyar nan haka kuma yana tsananin tausayinta sai dai duk yanda yaso da so da kaunar ta bai isa ba.....bai isa ba.”
Dagowa tai ta kalli madubin suka hada ido, kanta ta kawar sannan a hankali tace “Uncle!”
Yace “naam.”
Har zata cemai Goggo mahaifiyarta ce sai ta fasa, tace “shikenan ma.”
Yace “menene? Dan Allah ki fadamin.”
Shiru tai kafin can tace “Goggo nace a asibitin.”
Yace “nayi tunanin Goggon da kike maganar ta ne amma ya kuke?ni da nadauka ai Goggon mahaifiyarki ce.”
Zatai magana ya taka burki da karfi, juyowa yai ya kalleta yace “Jalila are u okay?”
Tace “eh menene?”
Yaran da suka tsallaka titin ya kalla yace “ yara ne wlh saura kiris su ja mana.”
Shiru tai batace komai ba, gangarawa asibitin yai, parking yai sannan yace “Jalila ki yi hakuri dan Allah.”
Kallansa tai tace “zancen hakuri da rashinsa ai ya kare, kafin ai abu ne ake neman canzashi ba bayan anyi ba.”
Ta bude motar sannan tace “nagode.”
So yake ya shiga amma bayasan ya kara bata mata rai.
Bata dade da shiga ba sai gatanan hankali a tashe tace “Uncle na rasa Goggo na.”
Sagir yace “ban gane ba?”
Kuka ta saka hankalinta a tashe take cewa sunce an mata transfer zuwa wani asibitin kuma basusan sunan asibitin.”
Yace “ban gane ba?”
Tana kuka tace “wai basu sani ba......”
********
Abba kam dakyar ya samu bacci jiya, ya rasa meyasa gaba daya tunanin yarinyar da bata fi sa’an dansa ba ya dameshi.
Ai kuwa da sassafe ya fada mota da driver dinsa suka nufo kano, ko kara bi ta contracts din baiyi ba.
Me ya sameshi? Me ke faruwa dashi?
*£**********
Mumy ce ta kalli Sultan tace “Sultan bari muje gidan Jalila, ko zakaje?”
Inna ce tai kakari wanda yake nuna mata ta daina, Mumy ta kalleshi tace “bari muje.”
Nan suka fito daga gidan suka shiga mota.
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*28*
Kasa tsayuwa tai kawai ta tsugunna agun tasa kuka, Sagir ya koma cikin asibitin ya tambayesu, yanda suka fadamai haka suka fada mai, fitowa yai gunta yace ta shiga mota tunda ai sunce wanda ya kawota shine ya dauketa