acece babbar ‘yarta ba, yo ai kowa yasan Safeena Qta fara haifa.
Hart takai matattakala uku sai ta tsaya cak tace “ba dai......?
Komawa tai da gudu saman ta bude dakin Inna, tace “Inna badai so kike ki cema mutane nice mahaifiyar Jalila ba?”
Inna bata kalleta ba sai shafa man zafin da takeyi a kafarta da takeyi, Mumy cikin mamaki ta karaso kusa da ita tace “Inna?”
Inna ta kalleta tace “ me? Kina tunanin is in possible?”
Mumy cikin tsoro tace “Inna me kike tunani? Taya zaki canzama yarinya mahaifiyarta? Bayan mahaifiyarta nanan da rai?”
Inna ta kalleta tace “ kina tunanin in Taura yasan gaskiyar al’amari akan ba yarinyarki bace zai yarda? Bakya tunanin zai ga yaudararsa mukai? In ya kwace kudin dayai investing a company dinmu fa saboda munyi betraying dinsa?”
Mumy tace “to ai bai fito filli yace ‘yata yakeso ba, shidai babbar yarinyar gidan nan yace, sannan in ta sanar dasu fa kafin kije? Ni Inna wannan karan ban amince da abinda kika tsara ba.”
Inna ta kalleta tace “shiyasa akoda yaushe nake ganin hankalinki da wayan ki na banza ne, ke wai haryanzu kina tunanin Abakar sanki yake?”
Tace “Inna zaki fara ko?”
Tufe maganin zafin tai tace “ kiyi gaggawar tashi daga baccin da kikeyi, kada ki kuskura kiyi relying akan kowa inba ni ba, sannan kada kiyi trusting din kowa inba ni ba.”
Mumy ta kalleta sannan ta mike kawai batace komai ba ta mike ta fito, itakam duk abinda Inna tace mata tana bi sai dai wannan karan hankalinta bai kwanta da hakan ba.
**********
Jalila kam da sutai sallar asuba falonsu na sama ta fito ta kwanta dan taga alamar baida niyyar mikewa daga gun.
Wajen karfe tara ta farka, jitai jikinta ya ware, saukowa tai daga kan kujerar data ke kwance sannan ta karaso jikin kofar, hannu tasa a hankali ta murda kofar, kanta ta zuro a hankali tana lekawa, bata ganshi akan gadon ba hakan yasa tai tunanin baya dakin, tura kofar tai shiga, tana shiga ta hangoshi a kwance akan sallaya inda yai sallah, baki tadan tabe tace “kamar gaske.”
Wucewa tai zata shiga toilet, gani tai ya fara wani abu harta je bakin toilet din, juyowa tai da sauri ta kalleshi, gani tai yana zufa sannan sai wani murkusus yake, idanunsa a rufe gam.
Kallansa ta sakeyi tace “mafarki yake?”
Kusa dashi taje tadan sa hannu tadan tabashi, hannunta ya rike da karfe yana wani irin numfashi, sankamewa taga yanayi, tsoro ne ya fara kamata, ga hannunta ya kankame da karfi wanda zafinshi ya isheta.
Cikin tsananin tsoro ta fara cewa “Yaya!” Dan abinda taji suna cemai kenan, Yaya! Yaya! A tsorace take kiran sunan nasa.
Ganin zufa tana keto mai ta ko ina ga sai kara kamewa yakeyi, yanzu kam hannunta ya saki yasa hannunsa a wuyansa yana kokarin jawo numfashinsa da yake mai wahalar shaka.
Jikinta ne ya fara rawa, ganin yanda yake sa hannu a wuyansa yasa tai saurin sa hannu ta rike nasa da karfi, a tsorace take cewa “Yaya! Yaya! Menene?”
Ganin abin karuwa yake yasa ta fara tofamai kulhuwallahu, falaqi da nasi, dan bata iya addo’oi ba.
Hannunta data rike nashi ya jawo hakan yasa ta fada jikinsa, da sauri ta mike, sannan ta shiga kiransa tana tabashi.
Ahankali yai wani dogon numfashi, sannan ya bude idanunsa wanda sukai jaa.
Idanunsa ne suka sauka a kanta tayi tsuru tsuru kamar kace mata kyaa ta ruga a guje....
Kallanta yai cikin rashin jin dadi, dan shikam yasan abinda yake tsoro kenan, bayasan wani ya ganshi cikin wannan halin.
Jalila kam tana nan a zaune kamar abu mara motsi har ya mike zaune, ganin yanda ta kame yasa ya mike tsaye ya zaune a bakin gado sannan yasa hannu ya shafi fuskarsa cikin takaici.
Jalila a hankali ta juyo ta kalleshi bakinta na rawa tace “ hmm ka ka......”
Kallanta yai fuskarsa a hade ga idanunsa sunyi jaa, wani irin tsoronsa ne ya kamata, gabanta ya shiga faduwa.
Idanunsa na kanta yace “ ka me?”
Kai ta girgiza da sauri tace “hm ba komai.”
Ta juya da sauri gaban wardrobe taje ta bude ta rasama me zatayi a kai sannan ta matso gaban madubi shima ta tsaya, sannan ta bude bandaki da sauri ta shiga ciki.
Duk abinda takeyi idanunsa na kanta, idanunsa ya sake runstewa cikin takaici, gani nai ya bude idanunsa ya mike da sauri ya dau waya da key din motarsa.
Yana kokarin fita itakuma tana fitowa, kallan juna sukai da sauri ya dauke kansa sannan yai waje.
Kallan kofar daya rufo tai sannan ta zauna a bakin gado tana maida numfashi kai kace gudu tai, me ke nan? Me ya faru dazu? Aljanu ne dashi? Kansa kalau kuwa? Badai wannan bace matsalar da Ummy tai magana?
Ta dade a zaune sannan ta mike tai wanka, haka ta sa kaya jiki a sanyeye sam hankalinta ya kasa kwanciya.
Ameera ce ta kwankwasa kofa, Jalila ta bude mata.
Tiren abinci ta miko mata tace “ga abincin yaya, ke kuma ki sako muje kasa.”
Jalila ta kalleta cikin sanyin jiki tace “Bayanan, sannan ni banajin yunwa.”
Ameera ta kalleta tace “yaza’ai kice bakyajin yunwa?”
Jalila ta kallet