fi.
Da sauri tace "Yahkuri yaya bansan kana nan ba."
Jalila ya kalla, itama kallansa tai sannan ta kalli Ameera, bata fahimceshi ba sai cewa tai "me zanyi?"
Hannu yasa ya turata waje sannan ya rufe kofarsa, Ameera ta kalla sannan ta kalli kofar tace "menai?"
Ameera tasa hannu ta jawota tana mata alamar tai shiru.
Suna sauka kan steps din tace "bayasan magana da hayaniya."
Jalila ta kalleta batace komai ba, haka suka sauka kasa.
Ummy nakan dinning tana rike da waya, kara neman number Abba takeyi amma shiru sai taita ringing harta katse ba'a dauka ba.
Sagir ne ya ajiye kular daya dauko daga kitchen yana cewa "Ummy haryanzu Abban bai dauka ba?"
Ta kalleshi tace "haryanzu, baka tunanin ko wani abun ya faru?"
Zama yai a kusa da ita yace "bakomai insha Allahu, maybe ko aikin dayaje yi ne ya rikeshi."
Su Ameera ne suka sauko, Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila ban yarda da kici abinci ke kadai ba dan ba lalai kice dayawa ba."
Jalila tai murmushi sannan ta zauna kusa da inda Ameera ta zauna.
Bata kula da Sagir ne a saitinta ba, sai da Ummy ta mika mata serving spoon.
Jalila ta amsa sannan ta kalli Sagir, idanunsu ne suka hadu da sauri ta maida kanta kasa, tana kallan plate din, ta ina zata ci abinci a nan?"
Ta dan zuba abincin kadan, Ummy ta kalleta tace "Jalila wannan dan abincin fa?"
Jalila ta kalleta tace "Ummy wlh haka cin abinci na yake."
Ameera tai dariya tace "irin cin abincin Yaya kenan, hmm kunyi anko."
Idanunta ta dago kadan ta kalli Sagir wanda yake ta juya abincin.
Shiru ne ya biyo bayan falon sai dan karar cokula da suke tashi, Ummy ta rasa me yasa gabanta ke ta faduwa.
Mikewa tai dan abincin da kyar take danci, ta kalli Ameera tace "ki dauko mata magungunanta tasha." Ta karasa maganar tana wucewa d'aki.
Ameera ta mike tai daki, ya rage daga shi sai ita agun, Sagir ya kalleta yace "Ya jikin naki?"
Bata kalleshi ba tace "na warke."
Shiru suka karayi yace "Jalilah....."
Ajiye cokalin tai da sauri sannan ta mike, dan batasan jin kalma daya daga gareshi, ina zata?
Nufar dakin Ameera kawai tai, Ameera na fitowa ta kalleta tace "ina zaki?"
Tace " hmm bandaki zan shiga."
Ameera ta mika mata maganin, amsa tai ta shiga ciki.
Tunda ta mike yake kallanta harta shiga, idanunsa ya rufe yana neman tsari daga sharrin zuciya, shikam ya san ya hakura sai dai yana san ya warware misunderstanding dake tsakaninsu.
*********
Acan Abuja kuwa Abba ne ya kalli abokin nasa yace "wai kai da mukazo yin signing contract me ya kawomu nan?"
Ya fada yana kallan wani gidan da abokin nasa yai parking.
Abokin nasa mai suna Hafiz ya kalleshi yace " abu zan amsa gun wani, yanzun nan zan fito.
Fitowa yai daga motar yabar Taura a ciki, tsaki taura yai shi ya kosa su gama ya koma masaukinsa dan ya manta da wayarsa garin sauri.
Sam bai kula ba sai jiyai ana kwankwasa glass din motarsa.
Zuge glass din yai tare da kallan windown, wani irin kamshi ne ya shiga ratsa cikin motar, kallanta yai yarinyace wacce batafi shekara 28 ba, fara ce wanda har farin nata ma yasa zakasan ba cikakiyar bahaushiya bace, kana ganinta zaka san irin matan nan ne shuwa.
Tasha kwalliya irin na zamani, kamshin da takeyi kuwa ba'a magana.
Ya rasa dalilin dayasa ya kasa dauke idanunsa daga kanta.
Murmushi tamai sannan tace "Yaya yace ka shigo kaci abinci."
Yace "Yaya?"
Tace "Eh ai mijin yayatane."
Yace "oh gidanshi ne kenan?"
Tace "eh."
Gani yai tasa hannu ta bude lock din cikin motar sannan ta bude kofar.
Kallanta yai, kayan da ke jikinta irin material ne mai kyalkyali, mace ce mai suna mace dan shape din ta ma abin kallo ne.
Kai ya girgiza da sauri dan shikam mace baiga kyan da zaisa ta rinjaye shi ba.
Kauda kansa yai daga kanta, matsowa tai saitin kunnensa tace "Please."
Baisan sanda ya mike ba yace "muje."
Gaba tai tana wani murmushi, dan dama wannan shirin sunfi wata biyar sunayinshi, tundaga sanda taganshi a Abuja yazo shida matarsa wani taro, kayan jikin matar kadai ta kalla tasan kudi ya zauna musu, data tambayi mijin yayarta shine ta karajin irin kudin da yake dashi.
Tun daga lokacin suka fara shirin jawoshi inda suke.
Haryasa kafa zai shiga sai ya tsaya, juyowa yai ya kalleta yace "kicemai yai hakuri inada abinyi."
Ya fada tare da juyowa tana mai magana bai tanka mata ba.
Motarsa ya shiga ya jata da sauri.
Ita kuwa Zaliha tana shiga cikin gida ta hade fuska, yayarta ta kalleta tace "ya ya?"
Kai ta girgiza mata kawai sannan ta wuce daki cikin takaici.
Yayarta ce ta kalli mijinta tace "Hafiz ya haka?"
Yace " Taura namiji ne da bai kallan matan waje kuna tunanin daga haduwa daya zai amince?"
Harararsa tai sannan tai gun kanwarta.
***********
Abba na koma wa dakinsa ya dau wayarsa, kiran Ummy ya sau goma, sannan yaga kiran Sagir sau biya, sai sauran wanda abune na aikinsa.
Yana shirin kiran Ummy wayar Hafiz ta shigo, dagawa yai cikin takaici yace "Hafiz bakada hankali ne?"
Hafiz yace "kayi hakuri dan Allah wl