, yana ji ta juya ta sauka, da kallo ya bitaa sannan yai ajiyar zuciya, dama ba auran ba, azomai da wasu sababbin al'amura shi ya tsana, sanda sukesan yai auran ba acemai komai ba, sai yanzu da yai auran ake san a canza mai rayuwarsa, me yasa basa duba yanayin lalurarsa tana bukatar sirri da kadaicewa?
Ameera bata samu Sagir ba, tazo ta sanar ma Ummy, ba tare da damuwa ba Ummy tace "a kai gobe, yanzu muje sama."
Tace "Sama kuma?"
Haka suka shiga d'akin Jalila tasa a kwaso kayanta, tayi mamaki sosai dataga duk an d'auke kayan lefen da suka sa mata masu tsadar ciki, sai dai bata nuna ma Ameera wani abu ba, Hassan na jin alamunsu yasan me suke shirinyi.
Fitowa yai ya sauko kasa ransa a bace zai fita.
Jalila ta fito dan neman yarinyar da batasan sunanta ba, tanaso tace mata ta nuna mata inda kayanta suke tanaso ta dauko abu (wanka take sanyi ga batasan inda inners dinta suke ba.)
Tana fitowa ta nufo falo tana tunanin inda zata ganta, tangamemen falon ta shiga kallo, dan dazu da yake kunya take sannan ba lafiya ce da ita ba ko kai bata daga ba, haka gidan yake? Kallan gidan ta shiga yi shi kuma ya sauko daga sama, san bata kuka dashi ba, shi kuma ransa a bace yake yana san fita.
Tana tafe shi kuma ya taho da karfinsa ya bigeta, tsoron faduwa yasa ta riko rigarsa suka fadi a tare.
Zafin faduwar ne yasa tai dan kara kadan, dagowa yai ya kalleta, itama kallansa tai.
Idanunta ne suka fito dan ta ganeshi shine na jiya, wato shine angon nata kenan, kura mata ido yai sosai wanda yasa ta tsarguwa.
A ina ya santa? Kallanta ya sakeyi, sannan ya mike tsaye.
Haushi ya kamata duk da batajin dadi ai yaci ace ya mata sannu dan ta tabbatar yasan ta bige sosai.
Hararsa tai wanda shi kuma daidai lokacin ya juyo da fuskarsa, hada ido sukai tana harararsa da sauri ta wayance tace "yaji ne ya shigarmin ido?" Wai ita adole bata ma kula dashi ba, magana take da kanta.
Hassan kallanta yai sannan ya tuno harararnan an masa ita sau biyu, har ya juya sai kuma ya kara juyowa yai ya kalleta dan ya fahimceta sosai, itace takan hanyarnan da wacce ta harareshi a adaidaita.
Oh, a ransa yace mai kuka?
Jalila ma shiru tai tana tunanin faduwarnan, bashakka ta tuno, da sauri ta d'ago ta kalleshi.
Mikewa tai tsaye, tana kokarin mai magana shikuma yai waje.
Da sauri tace " ba kai bane?"
Bai tsaya ba balle tasa ran tanka mata, kara kankance ido tai tana tunani, tabbas shine, wanda ya fadi akan titin nan.
Zata kara magana taga harya fita, da kallo ta bishi sannan ta dan tabe baki tace "ba dai sanda ya kusa kadeni ya sanni ba?"
Ganin batada amsar tambayarta yasa ta juya tana neman Ameera tare da rike bayanta, dan ta bugu sosai.
Ummy tasa aka matsar da kayansa bangare guda, sannan aka jerama Jalila nata, hatta kan madubi sai da aka matsar da kayansa akasa nata.
Ameera ta kalleta tace "Ummy kina tunanin Yaya zai barta kuwa?"
Ummy tai shiru, meye amfanin yi masa auran in basa tare?
Haka suka gama sannan suka sauko.
Jalila kam ganin ba alamar kowa yasa ta koma dakin ta zauna.
**********
A can gidansu Mumy kuwa, Dady na kwance yayi shiru, Mumy ta shigo dakin, kusa dashi ta zauna ta sakalo hannu ta gefen cikinsa ta rungumeshi tace "Dadyn Yasmeen tunanin me kake?"
Fuskarta ya shafa yace " Tunanin ki?"
Tace "ban yarda ba, tunanin Jalila kake?"
Yace "A'a why should i?"
Tace "karka boyemin komai plx, sannan kaima kaga gidan Taura ai, kasan daidai mata ne zasu samu zama a irin wannan gidan."
Yai murmushi, tace "yaushe za'a fadawa Goggonta?"
Yace "karki damu, ko ta sani yanzu ba abinda zata iyayi, macece mai hakuri, indai taga yarta cikin farinciki bazata iya cewa komai ba."
Mumy ta jinjina kai, yace "ya gun Safeena?"
Tace "suna Abujan, wai sai gobe zasuje ayi visa din."
Yace "okay."
#OneLuv๐
[08/10, 04:14] โช+234 803 380 9216โฌ: ๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*25*
Tana zama bata dade ba taji anyi knocking din kofar sannan taji ance "Ameera!"
Gabanta ne ya fadi jin muryar Uncle, wai nan fa gidansu ne ko? Sunanta Ameera dama?
A hankali tace "batanan."
Shiru yai shima kafin yace "Jalila dan bude."
Mikewa tai ta bude kofar ba tare da ta bari idanunsu sun hadu ba.
Sagir ya miko mata ledar dake hannunsa, kallansa tai bata amsa ba sannan batace komai ba.
Kallanta shima yake sannan yace " test din ya fito, shine sukaban magunguna, dama kinada typoid ne?"
Bata amsa mai ba ta amshi ledar ta bude, bayan magani taga yoghurt da exotic a kasa, zare ledar maganin tai sannan ta mikamai ledar kasan wanda ke dauke da yoghurt din.
Kallanta ya sake yi sannan yace "kinsan wasu basa san shan magani da ruwa shiyasa....."
Kallansa tai kamar zatai magana sai ta fasa, tace " Ameeran bansan inda tai ba."
Juyawa tai tana neman rufe kofar, hannu yasa da sauri ya rike kofar, juyowa