."
Mamaki ne ya kama Ameera wacece wannan da har batasan asan matsayin ta? Sai dai ba shakka suna tsananin kama, dan kamar ma harta baci.
Jalila ta kalli Ameera, Goggo ta kara kallanta tace "Allah sarki na gode sosai."
Ameera tace "bakomai."
Kallan Jalila tai tace "bari inje gun Ya Sagir."
Ta juya ta fita, tana rufe kofar ta kara bin kofar da kallo, tabbas dabadan ance yar Mumy bace da tace wannan ce mahaifiyarta.
Kwanciya Jalila tai a gefen Goggo dan tana jin jiki, Goggo ta shafi kanta tace " ki koma can ki kwanta dda kyau mana."
Jalila ta girgiza kai tace "barni anan."
Goggo ta kalleta tace " naji yarinyar nn tace Yaya Sagir? Ko Sagir din da ake bani labari?"
Jalila tai shiru dan batasan me zata ce ba.
Goggo tai murmushi, Jalila kam idanunfa ta rufe kawai, tana san sanar da mahaifiyarta sai dai tana tsoron kar jinjnta ya sake hawa, dan kuwa sanda aka kwantar da ita sai da akace a kiyaye sata a damuwa, wanda ta tabbatar in Goggo taji, ba magana kawai.....
Acan gidansu kuwa Hassan ya shigo cikin gida, Ummy na zaune afalo tai shiru.
Tsayawa yai yanasan mata magana kuma baisan ta inda zai fara ba.
Ganin bata da niyyar kallansa yasa ya juya jiki a sanyaye zai hau sama, jiyai tace "yanzu Hassan abinda kai ka kyauta min?"
Juyowa yai sannan ya matso kusa da ita, yace Ummy ni ban gane me na aikata ba.
Tace "kafi kowa sanin yanda matsala da lalurar cikin dare ke faruwa, taya zaka bar yarinya ita kadai a daki, yanzu inda ciwon ya gama cinta cikin dare fa?"
Yace "Ummy kinfi kowa sanin bana iya kwana da wani kusa dani....."
Tace " Hassan kanaso kace bakasan dalilin dayasa muka nemarma aure ba? Ko kuwa san kanka ne ya maka yawa da baka duba halin da nake ciki?"
Kallanta yai jiki a sanyaye, tace " akoda yaushe hankalina baya kwanciya da barin ka kai kadai a daki, saboda ina tsoron abinda zai iya faruwa, sannan yanzu an maka aure nan ma kace kai kadai zaka dinga kwana? Fad'amin Hassan menene marabarka da kafin kai auran?"
Kallanta yai sai dai baice komai ba.
Tace "In har na isa dakai na kuma isa in fadama kaji to daga yau inganku a d'aki daya, ban damu da duk abinda zai biyo baya ba sai dai jiya ya zama rana ta karshe da zaku kwana tare, sannan ko kunya ka barsu suka tafi asibiti kai ka shigo."
Yace "Ummy kinsan bana san asibiti."
Kallansa tai kamar zatai magana sai ta fasa, dolene subi komai a sannu tunda gaggawa ma aikin shedan ne.
****
Sagir ne ya kalli Ameera yace "ina kuma kuka je?"
Nan ta fadamai abinda ya faru, cikin mamaki yace "yanzu tana can?"
Tace "eh."
Sagir ya haura saman.
Jalila na kwance kusa da Goggo suka bude kofar tare da sallama.
Jalila na jinsa ya shigo, kallab Goggo yai sannan ya gaisheta.
Ta amsa fuska a sake tace "Malam Sagir ashe da rabon zan ganka?"
Dasauri Jalila ta d'ago ta mike tsaye tace "Goggo sai mun dawo."
Mamaki ne ya kama Sagir, ya mike yana cewa "ki zauna...."
Tace "muje kawai."
Sai da suka kai kofa sannan ta ma Goggo salama suka fita, suna sauka ta kan beni mai kula da Goggo tana hawa.
Gaisawa kawai sukai suka sauka.
An mata gwaje gwaje sannan aka bata magunguna, akace su jira a gama test, Ameera tace "Ya Sagir ka maidamu gida, kai ka dawo ka amsa."
#Oneluvπ
[08/10, 02:16] βͺ+234 803 222 1758β¬: π― *JALILAH* π―
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_π‘)
*I am really Proud of you! Can't believe Kainuwa has reach more than 300k views on wattpad, Heart U* πππππππ
*No 24*
Shiga d'aki yai ya tsaya yai shiru, tunani yake mai yai? Shi dai a iya saninsa baiga laifin da yai ba.
Bandaki ya shiga yai wanka, zama yai shiru, ga wunya da ta fara cinsa, yau Ummy mantawa dashi tai? Ko laifin daya mata ne yasa tai fishi dashi?
Kwanciya yai ya d'au jornal din da yake karantawa.
Jiyai yau karatun sam ba dadi, shi yace amai aure? Mikewa yai zaune sannan ya shafi fuskarsa, makullinsa ya d'auka da wayarsa ya fito, ba kowa a falon hakan yasa yai waje.
Yana kokarin shiga mota, su kuma suna shigowa.
Sai daya jira sukai parking sannan ya shiga mota ya tada ta.
Sagir ya fito da sauri yanasan mai magana, kafin ya karaso Hassan yaja motarsa yai gaba.
Sagir yabi motar da kallo, a ransa yace "anya nama Jalila adalci kuwa?"
Ameera ce ta bi motar sa da kallo sannan ta kalli Jalila ta mika mata hannu, Jalila tai murmushin yake sannan ta fito.
Ameera ta kamata suka shiga ciki.
Ummi najin motsin mota ta fito, tana kallan sanda Hassan yai waje, ga Abba tun safe yau ya tafi Abuja.
Suna isowa falon Ummy ta rike Jalila ta shigar da ita dakin Ameera tunda a kasa yake.
Ummy ta kalli Ameera tace "Ameera dauko abinci."
Nan Ameera ta fita, Jalila ta fara kokarin mikewa tana cewa "Ina kwana?"
Ummy tai saurin riketa tace "Karki damu, ma gaisa inkin ware."
Sagir na tsaye a jikin kofa yana murmushi, yasan halin Ummy ya tabbatar Jalil