dan zazzabin dake jikinta mai zafine.
Da kyar ta iya mikewa ta bude kofar, Mumy tace "Jalila ko wanka bakiyi ba? Naga tun jiya na ajiye miki kayan da zaki saka?"
Jalila ta kalleta bakinta na rawa tace " Mumy....."
Ganin yanda idanunta keyi yasa Mumy ta riketa, jitai jikinta ya d'au zafi sosai, tace "Zazzabi kike?"
Jalila tai shiru, hannunta ta kamo tace " Muje Inna ke nemanki, in ta gama miki magana sai ki dawo ki sha magani."
Nan ta rike hannunta suka fito, kallan banza kowa yake mata dan dama duk yan uwan Mumy ne masu tayata kishi da zuga ta.
Haka suka shiga d'akin Inna.
Tana zaune tana duba abu a waya suka shiga, sai data gama sannan ta ajiye ta kalli Jalila, sannan tai dialing number a wayarta tana cewa " magana zakuyi da Goggonki, ki sanar da ita baki da lafiya shiyasa ba zakizo ba."
Kafin Jalila tai kokarin bada amsa, har Inna ta miko mata wayar sannan tasa hands free.
Muryar Sultan taji yana cewa "Inna ina Jalilan? Gani a kusa da Goggon."
Jalila ta daure tace "Sultan ni ce."
Yace "Jalila Goggo na nemanki."
Ya fada tare da mikama Goggon waya.
Goggo na amsa tace "Jalila ina kika shiga?"
Jalila tace "Goggo zazzabi nakeyi shiyasa baki ganni ba."
Tace "ni ai dama cewa nai ki zauna ki huta, amma na rasa meyasa yau hankalina yake a tashe, dafatan ba abinda ya faru?"
Jalila tace "mai zai faru Goggo? Ke dai kawai kice ganina kikeso."
Goggo tai murmushi dan hankalinta ya kwanta tace "kinsha magani?"
"Eh Mumy ta kaini an banni magani."
Goggo tace "Ayya! To ki huta sosai, kar ki damu dani."
Jalila ta d'aga kai, idanunta suka ciciko a ranta tacce "Goggo ga yarki nan ana mata auran dole, auran fin karfi, auran mugunta, auran san zuciya...."
Jin shiru yasa Inna ta kashe wayar sannan ta kalli Jalila, hannunta ta kamo ta rike tace "good girl, karki damu ki kula da mijinki yanda ya kamata, muma zamu kuka da Goggonki yadda ya dace."
Jalila ta share hawayenta tace "Inna dan Allah ku kula da ita."
Inna tace " karki damu kanki, ai Goggo tamu ce, ke dai kiyi abinda muka saki."
Jalila ta d'aga kai alamar to.
Nan Mumy ta kamo hannunta suka fito.
Innata bisu da kallo, tabbas dolene su kula da Goggo sosai, saboda yanzu ne zasu kara bunkasa company ta hanyar Jalila.
Murmushi tai.........
Haka Jalila, Mumy tasata tai wanka, tasha magani, ta sa kaya sannan suka fito tare, gefe guda taja ta zauna.
Dan bata jin dadi, daga baya ma data kula hankalin kowa baya kanta ta zille tai bangarensu.
Kwanciya tai a inda Goggo take kwana, tana tuno rayuwar da sukai a cikin gidan.
Kuka ta shiga yi sosai, wanda ya kara sa mata ciwon kan dake damunta, sai yamma likis tana kokarin fita, Dady na turo kofar.
Kallanta yai jikinsa ne yai wani sanyi, yace "tundazu nake nemanki shine Mumyn Yasmeen tace kila kina nan."
Jalila ta kalleshi bata ce komai ba, kusa da ita ya zauna sannan ya kalli d'akin, yace "kina tuno rayuwa ne?"
Itadai batace komai ba, shiru ne yadan ratsa kafin yace "Jalila kiyi hakuri."
Kallansa tai cikin mamaki, yace "bazan nemi yafiya akan abubuwan dana aikata ba, domin har yanzu bana dana sanin aikata su, sannan abinda na aikata a baya sune suka sani nazama abinda na zama yanzu, sune kuma suka taimaka suka inganta rayuwar zuri'ata harda ke kanki, sai dai zan baki hakuri akan auran nan da aka miki dan kuwa na san bamu kyauta ba, sai dai ko yanzu aka dawo da hannun agoggo baya tabbas abinda zan sake yankewa kenan."
Kallansa kawai Jalila take cikin mamaki, dan ta kasa cewa komai, Dady yai shiru kafin yace "ki taso muje a shiryaki sun ce bayan isha'i zasuzo, dazu akaso kiranki nace a barki zuwa anjima."
Bata ce komai ba ta mike ta fita kawai, dan itakam bata san me zata cemai ba, tana koma tsoron kar bakincikin dake ranta yasa ta fadamai kalamai marasa dadi.
Haka ta wuce bangaren Mumy, wanka aka sata ta sakeyi tai sallah,sannan Mumy ta sata tadan ci abinci wanda cusa wa kawai tai, sannan ta bata magani, kayan da zata saka ta miko mata.
Haka Jalila ta saka kayan nan ba tare da tace kala ba.
Mumy ta mata kwalliya tai kyau sosai, turaruka ta fesa mata kala kala.
Mumy ta fita dan ance motoci sunzo.
Sagir na zaune a cikin mota gaba daya yau banda ruwa ba abinda ya shiga cikinsa, wace rayuwa zaiyi da Jalila a matsayin matar yayansa?
Gaba d'aya shikam yasan rayuwarsa ta gama hargitsewa.
Haka akai ta shiga motoci har aka fito da Jalila aka bude bayan motar da Sagir ya jawo wacce take ta Abba aka saka ta.
Kanta na kasa dan a lulube take da mayafi, tunda suka fito yake kallansu.
Jalila na zama taji yacema Mumy ina wuni?
Gabanta ne ya fadi jin muryar Uncle, shine zai ma kaita? Me yake nufi da ita?
Wani sabon takaici ne ya kara kamata, lalai yau ta tabbatar Uncle ba santa yakeyi ba.
Haka suka shiga motar aka ja, ita kadai ke kukanta, wanda kukan ke taba cikin zuciyarsa.
Haka sukai ta tafiya har suka isa makeken gidan.
Gabanta ne ya shiga faduwa sanda akace ta fito, wai yau itace aka ma aure da wanda ko sani batai ba, ko ka