nanta 10 kenan da zuwa gida wanda yai daidai da kwana 11 da kawo lefe.
Yau saura kwana uku kenan bikin ta amma bata sani ba.
Tana zaune bayan sunci abincin safe Sultan yazo shi da wata yarinya wacce batakai Jalila ba, gaida Goggo yai.
Jalila ta kalleshi tace "Sultan wannan fa?"
Yace "itace zata dinga tayaki zama, mai kula da Goggo."
Gabanta ne ya fadi dan tabbas ta fahimci me hakan yake nufi, yace "sannan Dady yanasan ganinki yanzu."
Jalila tai yake tana kallan Goggo, Goggo cikin mamaki tace "Allah sarki angode, kinga yanzu sai ki taimaka inkinje gida ki huta ki bari sai gobe ko jibi kya dawo tunda kinga jikin nawa ai da sauki sosai, ni da zasu sallamemu ma da naji dadi."
Jalila ta mike jiki a sanyaye, yarinyar ta gaida Goggo, Goggo ta amsa fuska a sake tace "ya sunanki?"
Zulai yarinyar ta fada.
Jalila ta matso kusa da Goggo ta rike hannunnta idanunta suna neman canzawa tace "Goggo sai na dawo."
Goggo ta jinjina kai tace "ki bari sai gobe ko jibi."
Tace to.
Haka suka fito ta shiga mota.
Suna fara tafiya ta kalli Sultan tace "Sultan wani abin ya faru ne?"
Yace "ban sani ba sai dai na tabbatar an kusa auranki tunda yanzu ma gidan da mutane, sannan naji Mumy na cewa an turo wai yau kanin Ango zaizo dan kuyi magana, tun jiya yaso zuwa to sai sukai tafiya, bandai san maganar da zakuyi ba."
Gaban Jalila ne ya shiga faduwa, a hankali hawaye suka fara zubo mata, kanin ango? Zancen me? Ankusa bikinta? Da wa? Wad'an nan sune suka sake ingizata ta shiga zubar da hawaye.
#Oneluv๐
[08/10, 02:12] โช+234 803 222 1758โฌ: ๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*No 20*
Suna isa gidan ta fara gaida bakin dake gidan, duk yan uwan Mumy ne dan dama a iya tsayin rayuwarta bata taba ganin dangin mahaifiyarta ba, dan duk yawansu ba mai nemansu, sannan shima Dadyn baya kuma san su nemeshin.
Shikuwa danginsa dama Mahaifinsa ya dade da rasuwa, sai mahaifiyarsa wacce dama ita kam bata san auransa da Goggo sai Mumy, takanzo lokaci zuwa lokaci, abinda zai baka mamaki shine, ita kadai take zuwa sai kanwarsa wacce dama ita fitsarariyace.
Ko sau d'aya Mahaifiyarsa bata taba cewa Innan Goggo tazo suje muhalin yarta ba, Jalila na shekara 10 Allah ya d'auki ran mahaifiyar Dadyn.
Shikadai yaje, dan sai daya dawo daga gaisuwa ya aiko mata da tsintsiya, kuka da gyada wai inji babarta sannan tasan yaje, sai Jalila data jiyo gun Safeena akan mahaifiyar Dady ta rasu.
Kaf gidan yan uwan Mumy ne, sai ita kanwar Dadyn ita kadai.
Abin mamaki shine taya akai tasan ana taro? Kuma me yasa itama in zata zo sai dai ta taho ita kadai? Kana ganin hakan kasan Dady ne ke sanar da ita.
Jalila itakam gaishesu kawai takeyi, tana gamawa ta mike zatai gun Mumy wacce ta leko tana mata alama da hannu akan tazo.
Jalila ta mike zata wuce taji an tawo mata hijab saura kadan ta fadi, kallanta tai zatai magana sai kuma ta fasa tace "Aunty?"
Kanwar Dady wato Aunty Adama tace "Ke dama bakida tarbiya, in ba haka ba ki gaida kowa baki ko kalleni ba?"
Jalila ta tsuguna tace "Aunty kema kinsan ban ganki bane."
Tace "eh ni da nake a kauye ai bazaki ganni ba, tunda kaf falon nan akaina idan naki ya makance."
Jalila zatai magana, Mumy tace "Jalila!"
Kallan Mumy tai sannan ta amsa, ta kalli Adama kafin tai magana ma tace "tashi kije ana kiranki."
Jalila ta mike ta wuce.
Tana shiga d'akin Mumy ta rufe kofa sannan ta riko hannunta.
Gefen gado ta zaunar da ita ta rike hannunta duka biyun tace "Jalila? Kinji abu kwatsam ko?"
Jalila ta kalleta idanunta sun canza kala tace "Mumy ban fahimci abinda ke faruwa ba."
Mumy ta rungumeta cikin murya mai rauni tace "Jalila nikaina abin nan na rasa ta ina zan fara sanar miki, dangin mijin ne suka ce suna san auran cikin gaggawa, yanzu nan da kwana uku za'a........."
Yanda ta ture Mumyn daga jikinta ne yasa Mumyn yin shiru, Jalila bakinta na rawa tace "kwana uku?"
Mumy tace "kiyi hakuri Jalila, sadaukarwa ce kikayi don ceto mahaifiyarki, kinfi kowa sanin Inna inhar bakiyi abinda tace ba, tabbas zata daina biya ma Goggo kudin asibiti ne, sannan zata iya korarku daga gidan nan, kinsan dai ba lafiya ne da ita ba, kar kuje garin wahala ciwon ya cita har azo ana dana sani...."
Wasu zafaffan hawaye ne suka zuboma Jalila, ta kara maimaitawa kwana uku?
Mumy tace " karki damu, mahaifinki ya yanke hukunci inhar akai auran kikaga ana cutar dake to ki sanar dashi shidakansa zai sa a raba auran."
Wayyo yarinta da rashin tunani mai zurfi yasa Jalila tace "Haka yace ?"
Mumy tace "sosai, kina tunanin zai bari a cutar dake ne?"
Shiru tai tana kallan Mumy, Mumy ta mike ta bude drawer ta d'auko mata wani dankararen material mai duwatsu, tace " ki tashi ki shirya, kaninsa zaizo yanzu, insha Allah Jalila ba abinda zai faru dake, kidinga sa mahaifiyarki agaban komai."
Jalila bakinta ma rawa tama kasa magana, Mumy ta