ubar da kwalla tace "Dady kaine mahaifina ko Inna?"
Cikin fada yace "Wai meke damunki ne?yaushe kika fara gardama haka? kina tunanin lalabakin da nakeyi zai baki damar bijirema abinda mukesanki dashi ne? inhar kinasan farincikin uwar data sha wahalarki, kina neman lafiyarta to kibi abinda muka ce miki sannan karki kuskura ki fada mata zancen nan."
Kallansa kawai take tana zubarda hawaye, faduwar da Goggo tai kenan su riba suka samu da rashin lafiyarta? tunda batasan dame zasuyi threatening dinta ba.
Dady ne yace "muje."
A hankali ta tura kofar ta fito, jitai kafafunta na rawa hakan yasa ta rike kofar motar.
Haka suka shiga cikin asibitin yana gaba tana baya.
********
A cikin asibitin kuwa Goggo ce tana kwance tana tunanin Jalila da bata dawo ba,Mumy ta turo kofar dakin.
Goggo ta kalleta sannan ta gaidata, dan dama tunda sukazo gidan haka suka saba, Goggo ce ke gaidata.
Mumy ta zauna a kan kujera sannan ta kalleta tace "Ya jikin?"
Goggo tace "Da sauki, tare kuke da Jalila ne?"
Mumy tace "eh suna tare da mahaifinta ne yanzu zata shigo."
Da sauri Goggo ta canza fuska tace "me yake ce mata? ba dai zance........."
Mumy ce ta katseta tana murmushi tace "Kai maman Jalila, ba wannan zancen bane, ai wannan maganar an ajiyeta sai kin samu lafiya, mun isa mu yanke hukunci ne mahaifiyar yarinya na asibiti?"
Goggo ta mata kallan zargi, Mumy tace "duk rashin kirkirnmu ai bamu isa yi mata aure dai kina asibiti ba, sannan mahaifinta ma har fada mukai akan zancen nan, ya hana a kara tada shi."
Jin hakan ne yasa Goggo tadan saki jiki har tace "mun gode kuna ta dawainiya."
Mumy a ranta tace "Yarki dai nayi.
Amma a fili tace " Karki damu, ke dai ki kwantar da hankalinki ki samu lafiya, kinga dai irin kudin da ake narkarwa a asibitin nan."
Turo kofar da Dady yai ne yasa ta dan canza fuska wai ita a dole fishi takeyi.
Jalila ta shigo ta tafi kusa da Goggo ta zauna.
Dady fuskarnan a hade yace "Ya jiki?"
Tace "Alhamdulila."
Kusa da ita ya matso ya ajiye mata kudi sannan ya juya.
Mumy ce ta mike tace "Sai an kawo abincin dare."
Goggo tace "Angode."
Haka suka fita, Jalila ta kwanta a kafadarta.
Goggo tace "Menene?"
Jalila ta kara gyarawa tace " Kawai dumin Goggona nakesan ji."
Goggo tai murmushi tace "wani abun ya faru ne?"
Tace " me zai faru? Ni fa bangarenmu naje na kwanta, hardasu barci."
Goggo tace "kin kyauta, ki dinga zuwa kema kina hutawa, zaman asibiti ba dadi sannan na kula bakya samun barci sosai."
Jalila ta daga kai tana murmushi.
Goggo ta miko mata duka kudin da Dady ya ajiye tace "irga."
Jalila ta irga tace "ni Goggo dubu ashirinn nake gani."
Goggo cikin mamaki tace "dubu ashirin? Me zamuyi da kudi haka? Sannan ni tunda nake a rayuwata ban taba rike kudi mai yawa haka ba."
Jalila a ranta tace " gashi kin rike yau tunda suna san saida farincikin yarki."
Goggo tai shiru aranta tana mamaki........
***********
A can gidansu Hassan kuwa, Sagir sai karya yai akan sunje sannan shima yayan ya ganta.
Ummy duk ta matso dasan jin labari tace "Sagir kana tunanin ta mai?"
Yace "kinsan halin yaya baice komai ba amma ga dukan alamu ta kwantamai."
Ummy tai murmushi tace "ni kaina nasan zata kwantamai dan wannan inaji a jikina alheri ne atattare da ita."
Abba yai dariya yace "Ah Alhamdulila lalai yau hankalinmu ya kwanta."
Hassan sai wajen magrib ya dawo, yana shigowa Ummy ta fito cikin farinciki tace "Hassan ka dawo?"
Kai ya daga kawai ya nufi sama.
Yana shiga daki, kafin kofar ta rufo Sagir ya shigo, yace "Yaya dan Allah me ka aikata dazu? Ta ya zaka tafi ka barmu a gidan yarinya?"
Hassan bai tanka mai ba sai rigarsa da ya cire dan dama ya gaji da ita.
Sagir yace "Amma Yaya wlh ba dadi, bakaji yanda na ji kunya ba, gashi an hada maka abinci kala kala.
Hassan ya juyo ya kalleshi, Sagir yace "Ya Hassan."
Hassan ya matso kusa dashi yace " Sry." Ya juya yaja towel ya shiga toilet.
Sagir ya bishi da kallo sannan yai ajiyar zuciya.
Juyawa yai ya koma d'aki, dan shi yau abin duniya shima ya dameshi.
Baiga Jalila a makaranta ba daya koma sannan duk yanda ya sake kiranta a waya sai acemai a kashe take.
*£*£*£££**
Ta kowani bangare shirin aure sukeyi, Sagir ya dawo kasa an kara gyara musu saman, sai dai duk yanda ake shirin auren nan Amarya da Ango ko a tsikar jikinsu, dan ita tana asibiti gun mahaifiyarta, yanzu ko gidan ma bata zuwa, kayanta kala uku data taho dasu shi take ta sawa.
Sam batasan auran sati biyu aka saba itadai kawai tasan batasan zuwa gidan ne ma bare a mata zancen.
Kudin da Dady ya basu shi suke dan kwalam dinsu, sai abinci da ake aiko musu, kaf gidan ba wanda ya sake zuwa duba Goggo sai Sultan da yake zuwa duk bayan kwana biyu, sannan ita ko lefen ma da aka kawo basu nuna mata ba, ita kuwa dama ba wannan bane a gabanta, bakincikinta inda zataga Ya Sagir.
Zuwanta makarantarsu uku amma ba ta taba dakar sa'ar ganinsa ba, har ta hakura.
A yau da yazone wanda kwa