samar maka abokiyar zama."
Hassan ya kalleshi yace " me kake nufi?"
Abba ya mike yace "Ka taimaka gobe kuje kai da Sagir, wannan rokone uba yake ma dansa."
Hassan yai shiru baice komai ba, fita Abba yai tare da rufe mai kofa, shiru Hassan yai yana tunanin wannan abun, shi gaba daya ya kasa hasko rayuwarshi da wata mace, macen ma wacce bai sani ba.
**********
Wajen karfe d'ayan dare ta mike daga kwanciyar datai dan dama ba bacci take ba, fitowa tai daga dakin ta zauna a kasan matatakalar benin, shiru tai tana tunani, ya zatai? Gaba daya duk yanda taso ta canza shawarar dake zuciyarta in ta auna lafiyar mahaifiyarta wacce ta rayu cikin bakin cikin da namiji bataji zata iya canza wata shawarar, rayuwar mahaifiyarta itace gaba da komai a rayuwarta.
Kanta ta kwantar akan gwiwowinta tana tunano rayuwar da sukai da Sagir da irin rayuwar da tai fa mafarkin yi dashi.
Wasu zafafan hawaye ne suke zubo mata, a wannan rana bacci baiga idanunta ba.
Wajen karfe 1o aka kawo musu abinci sannan drivern yace mata "Inna na jiranki."
Ta fahimci me yake nufi, kallan Goggo tai tace "Goggo zanje na kwaso kayan, akwai abinda kikeso?"
Nan ta fada mata abubuwan da takeso ta taho mata dashi, har zata fita sai ta dawo da sauri ta rungume Goggo idanunta na neman kawo kwalla.
Goggo tace "Jalila menene? Badai jiya karya kikamin ba? Ance miki wani abun a gidan ko?"
Dagowa tai tana dariya tace "Goggo kenan, kema kinsan bana iya boye miki komai a dunia, me zaisa in ki sanar dake? Inaji fa ganin kin kwanta yasa jikinsu yayi sanyi da zancen."
Goggo tai tsaki tace " duk yanda naso in zauna dasu lafiya in har suka sake suka miki zancen hadin aure wlh sai sunsha mamaki."
Jalila tace "ni inada ke a duniya me zaisa inji tsoro Goggona?"
Murmushi sukai a tare, Jalila ta juya ta fara takawa a hankali, daga sanda tasa kafa tabar dakin nan ta shiga motar ta tabbatar rayuwarta shikenan ta canza, bazatai dana sanin fita daga dakin nan ba kuwa?
Ai dana sani tun kafin ta fita tasan rayuwarta lalai tana cike da danasani, domin kuwa batasan wani irin zama zatai ba.
Sai data kai kofa ta juyo tama Goggo murmushi sannan ta fita.
Mota ta shiga tai shiru tana kallan waje, mutane take ta kallo kowa yana nasa rayuwar, haka har suka isa gidan.
Sai dayai kusan minti biyar da parking sannan ta bude kofar ta fito.
Inna ta kalli Mumy dake leken window ta dakinta, Mumy da sauri ta juyo tace "ta iso kuwa Inna."
Inna ta kalli Dady tace " sai ka kyautata mata kai kuma, ka tabbatar bata nunama mijin nata tsana ba."
Dady yace "to."
Mumy ta matso tace "Dadyn Yasmeen let us try our best."
Murmushi yai mata na dole sannan ya mike.
Inna tace " in zaku siyo ragowar kayan gida kudinga daukanta a asibiti."
Yace to, sannan yai waje.
Yana isa falon tana shigowa, tsayawa tai tana kallansa, wai mahaifinta? Wanda hakkinta ke rataye a wuyansa?
Dady ne ya matso kusa da ita, ya sa hannu a aljihunsa yace "Jalila ya mai jikin?"
Kallansa kawai take batace komai ba, sai idanunta da sukai ja, bata amsa mai ba.
Yace "me kike tunani?"
Kai ta girgiza alamar bakomai tace " kawai ina tunanin yanda Allah ya rataya wa uba hakkin dansa a wuyansa ne."
Dady yai shiru, zaiyi magana Mumy ta karaso tace "Jalila, yanzu muke shirin zuwa asibiti."
Jalila tai shiru a ranta tace "tunda kunsamu abinda kukeso ai dole."
Nan ta haura sama batare da tace komai ba.
Inna na zaune sai data zauna sannan tace "YA YA? Kin yanke shawarar?"
Jalila ta kalleta dan tana tsananin shakkarta ta daure tace "Amma kimin alkawari biyu."
Inna tace "inajinki."
Jalila tai shiru kafin tace " da farko zaku kula da Goggo, zaku samo mata wacce zata dinga taimaka mata, sannan na biyu karku fada mata komai har sai ta samu lafiya."
Inna tace "duk ba matsala bane, Jalila ta kalleta a ranta tace me zata samu da take bin ta kowace hanya dan ganin ta min auran nan?"
Dagowa tai da sauri datai tunanin wani abu tace "Inna tsoho ne?"
Inna tace "a'a saurayi ne"
Jalila cikin tsoro take kallanta, anya? Me suke tunani? In har ba wata matsalar mai zaisa su bar yarsu su zabeta?
Inna tace " ki tashi ki sauka kasa, bayan kinyi aanka kinci abinci ki shirya, ance bayan la'asar zaizo."
Jalila ta mike ta fito zuciyarta fal da tunani kala kala.
Bangarensu kawai ta nufa ta kwanta, karar wayarta taji.
Da sauri ta jawota, ta daga.
Muryar Uncle ne ya daki kunnenta, ji tai wasu zafaffan hawaye sun zubo mata.
Sagir yace "Jalila ina kika shiga haka? Ba dai wani abin bane ya faru ko?"
Kasa magana tai, hankalinsa ne ya tashi.
Ya shiga tambayarta, can ta daure tace "Uncle yaushe zamu hadu? Akwai maganar da zamuyi dakai."
Yace " ko yanzu ma in kinaso."
Tace "a'a banda yau."
Yace "nima na manta yau zan raka yayana wani gun, gobe fa?"
Tace " to, Allah ya kaimu, zan kiraka goben."
Haka kawai tace ta kashe wayar saboda yanda taji zuciyarta ta karye.
Tana kashewa kuwa tasa kuka.
Shikenan Uncle, soyayyar da muke ma juna