Jalila na zaune duba dan karatun da Goggo ta d'ora mata na islamiya, dan itama Goggon ba wani nisa karatun nata yai ba.
Goggo na kwance tana bacci, dan da safe sai da aka tsaga kafarta akai mata aiki, aka daye fatar gun aka wanke.
Amsa sallama tai sannan ta kalli kofar, Sultan ne ya shigo ya ajiye kular abinci sannan ya kalleta yace "ya mai jikin?"
Tace da sauki Sultan.
Yace "Inna na san ganinki."
Tace "akan me?"
Ta fada tana kallan Goggo, ganin tana motsi yasa ta mike da sauri ta kamo Sultan suka fito, tace "akan me?"
Yace "ban sani ba wlh, amma jiya dai naga mata sunzo da akwatuna, naji kuma ana cewa naki ne."
Tace "Mene?"
Shiru yai ganin yanda tai, yace " menene? Baki sani ba?"
Idanunta ne ya ciciko tace "Sultan zaka iya zama agun Goggo naje na dawo?"
Yace " ba matsala."
Tace"nagode Sultan, dan Allah ko ta tambaya kace mata naje gida dauko kaya ne."
Ya daga ai.
Mota ta shiga drivern ya ja, tunda ta shiga jikinta ke rawa har suka isa.
Haka ta fito da kyar ta shiga cikin gidan.
Yasmeen na falo ita da Mumy, gaishesu kawai tai ta wuce.
Inna na zaune ta shiga, sai da ta zauna sannan ta gaisheta.
Bata amsa ba ta ajiye mata farar takarda a gabanta.
Jalilata kalleta tace "Na menene?"
Inna tace " duba ki gani."
Jalila ta sa hannu ta dauka, receipt ne da aka bada a cashier, ga kuma tambarin asibitin Standard a jiki.
Kallan Inna ta sake yi, Inna tace " Bakiyi makaranta bane?"
Jalila ta kara kallan takardar, kudi ne zunzurutu wanda aka biya, na daki da kuma na aikin da aka mata da na treatment, sa dai bataji su a gunsu kudi ne mai yawa.
Kallan Inna ta sakeyi dan bata fahimci me takesan nuna mata ba.
Inna tace takardar kudin da muka kashema Mahaifiyarki ne.
Jalila tace "na gani angode Allah ya saka....."
Inna tace " Biya zakiyi."
Jalila cikin rashin fahimta tace "bangane ba."
Inna tace "kina tunanin kina zaune a gidan mu, mun saki a makaranta, mun kula dake da mahaifiyarki, mun biya mata wannan kudin, sannan kice ba zakibi umarnin mu ba?"
Jalila tace "Inna......."
Inna ta katseta tace "yaya? Kina da kudin da zaki biya mu dai ko?"
Idanunta ne suka kara firfitowa ta fara zubarda hawaye, Inna tace " in har kinfi karfin bin umarninmu sai mu zare hannunmu daga rayuwarku sai inga yanda zakuyi, ina fatan kinada inda zaku zauna da kuma kudin da zaki cigaba da kula da mahaifiyarki harta warke."
Jalila tasa kuka tace "Inna dan Allah kiyi hakuri, Goggo tana neman kulawarku dan Allah ki yafemin."
Inna ta mike tace " tashi ki fita, na baki daga yau zuwa gobe da safe inhar baki bi umarnin mu ba, zansa a koreta daga asibitin, sannan kubar gidan mu bayan kin biya kudin."
Jalila ta zauna tana wani irin kuka mai ban tausayi, Inna tace "tashi ki fita."
Mikewa tai tana hawaye ta sauko.
Yasmeen na mata magana ko kallanta batai ba ta fito tana hawaye.
Bangarensu ta nufa kawai ta zube akasa tana kuka, ya zatai? Uncle ne ya fado mata, da sauri ta janyo jakarta ta zaro wayar nan.
Ganin irin kiran da yai mata yasa ta saurin danna kira, ringing take ta yi ba'a daga ba.
Shikuwa a lokacin Ummy ta nemi ya rakata store, sai daya shiga mota ya tuna yabar wayarsa a gida.
Sai dai ganin ba wani dadewa zasuyi ba yasa ya fita kawai.
Kuka ta shiga yi sosai da taga bai daga ba, kira take tayi ba kakkautawa.
Ganin ba dama ta cila wayar kan gado ta fito rike da jakarta.
Tana tafe tana kuka, drivern na mata magana ko bi takansa batai ba tai waje.
Tana tafe tana wani irin kuka.
Sai da ta mike layinsu sosai, taje tsalakawa ta titi shi kuma ya taho saura kiris ya bugeta, wani irin burki yaja da karfi sannan ya kifa kansa da sitiyari.
Jikinsa ne ya shiga karkarwa, Jalila kuwa ta dauka karshen rayuwarta yazo har ta tsugunna, ganin bai kade ta ba kawai sai taji wani irin kuka yazo mata.
Tsananin tsoro yasa zufa ta shiga keto mai, da kyar ya iya fitowa daga motar, kusa da ita yazo yanda yaji tana kuka yasa yaji kansa na wani irin juyawa, dan tabbas ya dauka ya mata illa, dan uwansa ya hango alokacin da matsalar da bazai taba mantawa ba ta faru, numfashinsa ne ya shiga sarkewa, hannunsa yasa a wuyansa yana wani irin abu.
Jalila ta dago, ganin mutum na neman zubewa yasa hankalinta ya tashi.
Da sauri ta shiga yin ihun neman taimako.
Mikewa tai zata nemo mutane, hannu yasa ya riko siket dinta.
Juyowa tai da sauri tare da tsorata.
Da kyar yace " ba bige nai ba?"
Gaba daya ta tsorata dan ta dauka shi aka bige.
Siket dinta ta fizge ta tsaya tana kallan sa.
Mikewa yai sannan ya matso kusa da ita, matsawa ta dan yi.
Ya kara matsowa fuskarsa a hade, kara matsawa tai cikin tsoro.
Yace " meye dalilinki na tsugunnawa akasan motata da sa mun kuka?"
Jalila ta kalleshi tace " motarka ce?"
Yace "tambayarki nake?"
Ta kara kallan motar sannan ta tuno abinda ya faru da irin mai motar, da alama duk masu irin motar nan basuda mutunci.
Tace " na dauka ma hakuri zaka bani, tunda kasan na tsorata."
Baya san magana amma ya