aifinta yace a'a sannan ya sanar dashi ya daukoni ya dawo dani boys Quaters.
Fatima tasha bori balle da taji inada ciki wanda itama a lokacin tanada ciki.
Haka ya sata a daki ya dinga lallabata har ta yarda sannan ya mata alkawarin bazai kara shiga dakina da sunan tarayyar aure ba.
Zinaru kuwa tasha mita sai dai ba yanda zatai saboda umarnine na mijinta.
Wannan shine dalilina na komawa gidan, mahaifinta shine ya sa miki suna Jalila bayan an sa miki asalin sunan mahaifin Habubakar.....
Kuka ne ya ci karfin Jalila wacce bakin ciki da takaici sukama yawa............
Goggo tace "Jalila bana ganin laifin mahaifinki domin tun farko ya nuna bayaso, iyayena sune basu damu da rayuwata ba...
Jalila cikin kuka tace "kowa nada laifi Goggo ta ya za'a maida rayuwarki kamar rayuwar dabba?ta ya ta ya............
Kuka ne yaci karfinta wanda ya hanata magana...
#Oneluv๐
[08/10, 02:07] โช+234 803 222 1758โฌ: ๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*No 16*
Kallansa Inna tai sannan ta zare tabaron dake manne a fuskarta, ta ajiye magazine din da take dubawa tace "Me kace?"
Abubakar ya kalleta cikin jin shakarta yace "Inna abinda akai dazu bai daceba, bana tunanin ya kamata a sa rayuwar mahaifiyarta a tsakiya saboda neman abinda mukeso."
Inna tai murmushi sannan tace " a yau ne ka fara damuwa da yar taka? Ko kuwa yau ne kake neman kula da matarka?"
Yace "Inna kinsan ba haka nake nufiba."
Tace "ya isheni haka nan, sannan daga wannan lokacin ba ruwanka akan duk abinda na sharada akan harkar bikin nan, na dauka kaine ka sanar damu da matar da abinda ke cikinta duk baka sansu? Na dauka kaine ka nuna mana Fatima da 'ya'yanta ne kadai abinda kake so?"
Yace "Inna......"
Tace "ya isheni haka nan."
Mumy cikin rashin jin dadi tace "Inna me yasa kike san canza maganar mutunci zuwa rashinsa? Kinfi kowa sanin Abban Yasmin ba haka yake nufi ba, ko ni banji dadin abinda kika aikata ba dazu, yanzu da tsautsayi yazo da mutuwa fa?"
Inna tace "kin min shiru ke kuma ko kuwa?"
Mumy tai shiru, Inna ta kalli Abubakar tace "zanyima tambaya ta farko kuma ta karshe akan harkar Jalila, da ita da company dinmu wanne kake ganin yafi cancanta a ceta?"
Dady ya kalleta jiki a sanyaye, tace "ina jinka."
Yace " ba dogon nazari Inna kinsan company yafi, sai dai......."
Tace "magana ta kare, daga yanzu kuma daga kai har Fatima sai ku bar komai a hanuna, yarinyar nan dai ba gidan yankan kai zamu kaita ba, ba gidan yan shaye shaye ko talakawa zata ba, mezaisa kudinga haka?"
Dady da Mumy sukai shiru, can tace "ina takardar asibitin?"
Dady ya zaro a aljihu ya mika mata, nan suka fito.
Dady na shiga daki ya zauna a bakin gado ya shafi fuskarsa sannan yai wani irin ajiyar zuciya.
Kusa dashi Mumy taje kusa dashi ta zauna, tasa hannunta a kafarsa.
Hannunsa ya sa ya zare hannunta daga jikinsa yace "Fatima duk yanda naso nai tunani akan abin nan i think this is not right."
Hannunsa ta kamo tace " let us save the company first, in komai ya daidaita sai musan ya zamuyi da Jalila, karka damu."
Kai ya daga alamar gamsuwa, sannan ta jawoshi jikinta ta rungume.
Shiru yai yana tunani, tabbas company dinsu shine darajarsu sai dai idanun Jalila sun tsaya mai a rai.
*********
Yau duk yanda taso tai bacci ta kasa, juyi kawai take tana kara karanto rayuwar mahaifiyarta, tabbas dolene yanzu ta dau damarar taimakon mahaifiyarta, insha Allahu yau ne rana ta karshe da Mahaifiyarta zata zubar da hawaye, tunda a tsawon rayuwarta ta kula rabi na bakinciki da zubar da kwalla ne, sai dai ta yaya zata temaki mahaifiyarta?
Hawayenta ta share, kalaman Inna ne suka sake dawo mata, haka tai ta juyi har batasan sanda bacci yai gaba da ita ba.
******
Washegari Ummy bayan anyi sallar azahar ta fito da lefe dan kara dubawa ita da yan uwanta, Ameera na ta zungurin Aina'u dan tasan Aina'u na san Hassan.
Aina'u tai murmushi kawai ta mike tai ciki.
Hassan kam dama tunda ya fara jin hayaniyar mutane ya bar gidan, da Sagir akai ta hidimomin.
Bayan la'asar aka kawo lefe gidansu Jalila, yan uwan Mumy me suka karbi lefen, ganin uban kayan da aka kawo, dan akwati set biyu aka kawo masu dan karen kyau da tsada, sannan kayan dake ciki, ba'a magana, yan uwan Mumy sukai ta mata fada akan ta bark dan masu kudi yaso yar da ke zaune a gidansu a maimakon yarta, in taji haka murmushi kawai take sai tace wai ai so ba ayi masa dole.
Haka yan kawo lefe suka tafi bayan an tsaida biki sati biyu.
Ameera ce ta sanar ma Mumy cewa Ummy tace angon zai zo gobe dan yaga Amarya.
Ana watsewa Mumy ta hau sama da sauri ta sanarma Inna.
Ganin abin bai damu Inna ba tace "Inna kina tunanin Jalilan zata yarda taje?
Inna tace " ki tura mota a daukomin Jalila zanyi magana da ita."
Mumy tace "me zakice mata?"
Inna tace "ba ruwanki, ke dai ki yi abinda nace."
Mumy ta mike ta fita.