aru tai ta rabasu abin yaci tura, shi kuwa Abbakar ya dinga riricema Fatima akan kaunar da yake mata.
Fatima taki ci taki sha ita fa sai Abbakar, mahaifinta shikam dama yana so, Zinaru kuwa ganin abin na Fatima yayi nisa dolene ta amince amma da sharadin dolene ya zauna dasu sannan ya cigaba da karatunsa, sannan duk abinda ta unarceshi dolene yayi.
Abbakar hankalinsa ya kwanta dan yanzu yasan tabbas ya zama wani abun, Mahaifin Fatima ne yace yaje gida ya sanar ma iyayensa.
Sam Abbakar baiso ba danshi babu komawa kauyensu a tsarinsa.
Haka ya shirya ba'a san ransa ba yace zai taho, key din motarta Fatima ta bashi tace yaje da ita dan ya dawo da wuri.
A yanzu shekaruna 18 duk garin har iyayena sun gallabeni gashi mahaifin Habubakar yaki yarda a hadani da wani, a lokacin akwai wani babban mutun wanda yakeda mata biyu dayaso ya aureni amma yaki.
Haka rayuwata ta koma cikin tsangwama da wulakanci a garin, kuka kuwa nayishi har ba iyaka.
Kwatsam ranar mahaifina ya shigo cikin farinciki yake cewa Habubakar ya dawo.
Sam ko mikewa banyiba daga aikin da nakeyi saboda ni maganar mutunci ma bata taba hadamu ba.
Randa Ya isa gidansu mahaifinsa ya haushi da fada ta ko ina bai ma jira maganarsa ba, sannan yace a ranar zai daura mana aure.
Ran Habubakar ya baci sosai yace shi ba wanda ya isa ya aura mai yar kauye, haka aka turo gidanmu akan washegari da azahar za'a daura auranmu.
Bakin ciki yasa Habubakar ya fita can bayan gari gidan wani tsohon abokinsa inda suke zama da yaje ya aika a kirani.
Da kamar bazanje ba tsautsayi yasa na fita, haka yaran dan aiken ya kaini har gidan.
Tsayawa nai a waje saboda bansan dakin ba.
Habubakar ya bude kofar yasa hannu ya fizgoni ciki, ba abinda yacemin sai gefe daya koma ya cigaba da cin abinsa yana dadana waya.
Na gaji da tsayuwa haka Yasa nace zan tafi.
Mikewa yai yazo kusa dani yace " ni kike jira na aureki? Na miki kala da dan garin nan? Ko mijin wata kuchaka kamarki?"
Nace "naji koma menene ni ba damuwa amma kabarni na fita."
Dariya yai sannan ya sa abu ya rufe kofar ya koma yai zamansa.
Kafafuwana har suka gaji suka fara rawa saboda tsayuwa, nan fara kokarin bude kofar ji nai an fizgemin hijab dina ta baya an yar a kasa, tsoro yasa na fara kuka ina matsawa.
Dariya yamin sannan ya koma ya zauna, baifi minti biyu da zama ba mukaji ana buga kofa da karfi, muryar mahaifina da mahaifinsa mukaji suna cewa Habubakar ka bude kofar nan ko kuwa?
Mamaki ne ya kamani da naga ya cire rigarsa ya bar vest sannan ya taso ya bude kofar.
Yana budewa ya koma gefen kafita yana cewa Baffa kayi hakuri.
Nikam hawaye na nacigaba dayi, ganin abinda ke faruwa yana zuwamin a baibai.
Mahaifina na zuwa ya kwadamin mari ya fara makamin kafa, nan na hau kuka sosai.
Mahaifinsa ma ya hau dukanshi, yan kauyenmu na waje suna gulma.
Kuka kuwa kamar zan mutu haka na dinga yinshi.
Kallansa nai nace "Habubakar ka hadamusu gaskiya ni wlh ba abinda nai."
Mamaki ne ya kamani da naga ya min dariya ta kasa, anan ne na fahimci shiri ne nashi.
Nan na shiga yin kuka, shikuwa ya dauka in yai haka mahaifina zaisa a hanashi ni, baisan suma duk sun gaji dani ba, haka suka dauramana aure bayan sallar asuba wanda tunda muke a kauyen ranarce ana ta farko da aka taba yiwa mace aure da asubahi.
Ranar dukan da na sha ba'a magana, Habubakar kam bakin ciki kamar ya kasheshi.
Yaso guduwa da asuba amma yaji an rufe kofarsa, haka yana ji yana gani aka hanashi fita.
A ranar da rana aka kawoni ba tare da wasu kayan daki ba, kuka kuwa nayishi kamar in kashe kaina.
Shikuwa bakin cikin an hadamu daki daya yasa ya huce a kaina wai ai ni matarsa ce.
Wannan ita kadaice ranar da wani abu ya shiga tsakanina dashi, sannan itace ranar da aka samu cikin ki.
Inna ta goge wata kwalla wacce ta zubo mata, tace haka aka sashi dole ya tafi dani, naje gida sallama sai mahaifina cemin yai duk randa na tako garin nan ba tare da Habubakar ba bazai taba yafemin ba, ya kuma fadi haka ne har bayan ransa.
Innata ma ta kara jaddadamin hakan, haka aka sani a motarshi a dole yaja muka tafi.
A hanya sai wayarsa yakeyi da Fatima, yana gamawa ya hau ni da masifa akan shi a duniya ba abinda ya sani sai kansa, sannan duk abinda zai aikata sai dai yai abinda yasan zai amfaneshe.
Haka ya kaini can wata unguwa wanda ya kamamin gidan haya daki daya ya sani, sannan ya bani kudi.
Tundaga ranar ban kara sashi a idona ba sai dai lokaci lokaci wani yaro yana kawomin kudi wanda nake sana'a.
Shikuwa sunyi auransu da matarsa suna shan soyayyarsu.
Gidan hayar kullum habaici sukemin akan cikin shege ne a jikina.
Cikina ya kai kusan wata bakwai abin duniya ya dameni, sai ranar kwatsam Habubakar yazo.
Baiyi mamakin ganina da ciki ba, sai dai baice min komai ba ya ajiye abinda ya kawo ya fita.
Ashe gidansu yaje ya sanarma mahaifin Fatima hadin auran dolen da akamai da cikin da nake dashi, ya karasa maganar yana kuka yana cewa shi in har Fatima tace ya sakeni to ba wani kokonto zau sakeni ne.
Mah