yai shiru dan kansa har yanzu yana sarawa, yace "naji kiyi duk abinda kike ganin shine daidai."
Ya fada tare da fita daga dakin, da kallo ta bishi dashi cikin tausayawa, dan tasan halin zuciyar danta, mutum ne mai saukin kai, sai dai tundaga faruwar al'amarin nan ya rikede ya koma haka.
Hassan na fita ya fizge mota yai gaba.
Jalila kuwa da daddare Driver ya kawo musu abinci, ganin yunwa zataata lahani ne ya sa ta zuba abincin taci.
Goggo ce ta farka daga nannauyan maganin baccin da aka sa mata, kallan Jalila tai sannan ta kalli asibitin, a hankali ta budi baki tace "Jalila!"
Tsame hannunta tai da sauri ta isa guda da ita tace "Goggo! Kin ganeni?"
Da kyar ta mata murmushi tace "Jalila karki kuskura ki yarda da abinda Mahaifinki ke shirin yi miki."
Jalila ta kalli kasa jiki a sanyaye sannan ta kalli Goggo tace "Goggo abinda kikesan cemin kenan daga farfadowarki?"
Goggo da kyar tace "Karki yarda Jalila, bazan kara bari su cutar dake ba ta hanyar da bazata kare ba, aure ai ba wasa bane."
Jalila tace "to bazan yarda ba yanzu dai ki kwantar da hankalinki kinji?"
Goggo ta daga kai a hankali, wani baccin ne ya kara yin gaba da ita.........
#ONELUV💕
[08/10, 02:05] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*No 15*
Wajen karfe 12 na dare tana zaune akan kujera a kusa da mahaifiyarta ta kwantar da kanta a kusa da ita, Goggo ce ta bude idanunta a hankali tare da kokarin yin motsi da hannunta, Jalila cr ta farka wanda dama tana rike da hannun Goggo gam.
Tace "Goggo jikin ne?"
Goggo ta girgiza kai ta mata alama data kwanta a kusa da ita sannan ta matsa mata, Jalila tace "ya za'ai in kwanta anan Goggo? Ki bari zan kwanta a kasa."
Goggo tace "kwanta anan mmagana zamuyi."
Jalila ta mike ta kwanta akan karamin gadon wanda ya musu kadan, Goggo ta rike hannunta tace "Jalila duk abinda zai faru karki yarda da abinda mahaifinki ke shirin yi miki, daga shi har zuri'arsa, kinada wanda kikeso dan haka ni mahaifiyarki na baki shawarar bin zuciyarki."
Jalila cikin sanyin murya tace "Goggo me yasa muke zaune a cikin mutanen da basa kaunarmu?basu damu da rayuwarmu ba?"
Goggo idanunta suka canza kala zuwa damuwa da bakin ciki tace" Sunana kamar yanda kika sani Khadija, amma Kubra ake cemin, muna zaune a can wani kauye mai suna Chabai wanda yake karkashin karamar hukumar Misau a gariin bauchi.
Kasancewar karamin kauye ne sannan haka al'ada ta saba yarinya tun tana tsuma ake mata miji, haka zata taso har lokacin da zata isa aure a aura mata shi.
Mahaifiyata itace mace ta uku a cikin matan mahaifina, sannan itace ta tsakiya, 'ya'yan gidanmu mu 23 ne, nice ta 5 sannan ta biyu a gun mahaifiyata, a ranar da ake radamin suna a ranar ne Mai garin mu wanda ya kasance mahaifin Habubakar yamai kamu na.
Na taso mace marasan hayaniya dan a garin yara sa'anina har tsiya sukemin saboda asaranci irin nawa da rashin iya fada, Habubakar kuwa mutun ne dan gayu wanda tunda ya tasa yake bin yan garinmu Misau, Lagos da kano in zasu tafi rani.
Ko sau daya bamu taba kebancewa da sunan saurayi da budurwa ba saboda shi gani yake yafi karfina, sannan sam baima fiya zama a garin ba.
Ya yawan kasuwancinsa ne ya hadu da wani babban mutum mai kudi a garin kano, wanda suke safarar kayan abinci.
Habubakar nada kokari da himmar yin aiki shiyasa mutumin ya amince dashi sannan yasan harkar gona sosai, ganin yana moruwa da Habubakar ne yasa mutumin ya nemi shawararsa akan sa shi yayi karatu, haka Habubakar ya shiga makaranta ba tare da ya sanar a gida ba, a aji hudu aka sashi saboda girmansa, ya dage sosai saboda shi mutum ne mai tsananin buri da san ya zama wani abun, haka ya share sama da shekara 8 a garinkano yana harkokin karatunsa da taimakon Uban gidansa.
Sam ba abinda ya dameshi da tushensa inda iyayensa suke.
Ni kuwa a lokacin sa'anina duk sunyi aure dan alokacin shekarata 15 duk inda naji tsiya akemin akan nayi kwantai, hakan yasa ko fita nadainayi, sannan Innata ta ma daina bani talla dan haushi ma takeji itama akan kullum ta bani tallan kunu kwantai yakeyi.
Shi kuwa Habubakar ya zama dan gayu yana ta hidimominsa, alokacin ne kuma Mumy taji kaunar Habubakar ma ratsata saboda duk wani abu datake so kafin ta nema zakaga ya mata shi, wanda shi a gunsa ba wai so bane tsabar neman gun zama ne a gidan.
Mumy wanda asalin sunanta Fatima ta bayanna ma Habubakar san da take mai,ba wani kokonto ya amince da ita saboda a lokacin ne ya tabbatar da arzikinsa ya tabbata.
Haka ya dinga nuna mata tsantsar kauna ba tare da sanin iyayenta ba, Fatima tayi zurfi a kaunar Abbakar wanda ya canzama kansa suna zuwa na gayu.
Hajiya Zinaru wacce take mahaifiyarta ta mata hadin aure da dan uwanta, sai dai Fatima ta sanar dashi bata san sa ita Abubakar take so kuma zata aura.
Alokacin ne akan san da soyayyar dake tsakaninsu, duk yanda Zin