llan Mumy tai tace " yaushe kike tunanin ya kamata asanar mata?"
Mumy tace " duk sanda ya dace kinsan bata isa bijirema maganar mu ba tunda tasan Uwarta a karkashinmu take, sannan in muka mata barazana da rayuwar ta ba shiri zata aminta da duk abinda muka gindaya mata."
Inna ta jinjina kai tace " hakan yayi, yanzu mu bari sai jibinbin ankawo lefe dan na tabbatar bazai wuce sati biyu ba bikin dan da alama Taura ya kosa."
Mumy tace "mu ko yau yake so menene damuwar mu? Shiyasa ma nace Safeena ta cigaba da zama a gidan kawu daga nan ta wuce Egypt hankali a kwance."
Inna tace " da nace kibi mijinki Abuja yau kin binsa kikai ko?"
Tace "Inna dan Allah ki kyale Abbakar, sai yaushe ne zaki barshi yai aikinsa cikin nutsuwa?"
Inna ta girgiza kai tace "haryanzu baki da hankali, ke wai a naki haukar har yanzu kina tunani tsabar so ne yasa yake kula dake haka? Yake kuma wulakanta matarcan?"
Mumy tace "Hajiya."
Inna tai tsaki tace "Ke kika sani, ni dai company din ku bazan taba yarda na barmai gaba daya ba dan kina kallan idanunsa da yanda yake aiki zakisan akwai tsantsar greediness."
Mumy ta mike tace " Zan sauka."
Inna ta kalleta ta girgiza kai, tace ba da dan ina nuna mai matsayinsa ba kina tunanin zai ci. A da darajaki ne?"
Mumy tai shiru, Inna tace "jeki ke kika sani."
Mumy ta sauko ranta ba dadi.
*******
Ummy ce ta turo kofarsa dan tajita ba a kulle ba, yana zaune a kasa yayi shiru sai ma ka rasa me yakeyi shi kadai kullum a zaune, ta shiga ta ajiye tiren abincin sannan ta zauna gefensa kadan tace "tunani kake?"
Kallanta yai bai ce komai ba, tace "Dazu Abbanka yama magana ko?"
Yanzun ma baice komai ba, tace "Hassan mu iyayenka ne wandanda duk duniya duk wani mai sanka sai dai ya biyo bayanmu, ka fi kowa sanin bazamu zabama abinda zai cutar dakai ba, bazan kuma nemi takura maka ba, sai dai abu daya zan fadama wannan auran ni na fara amincewa akai sannan shine babban burina wanda nakesan ka taimaka ka cikamin shi."
Ta danyi shiru kafin ta mike tai waje.
Da kallo yabi bayanta sannan ya runtse idanunsa, Ummy ya takeso yai?
#ONELUV💕
[07/10, 22:19] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*Sisters Always Ask Questions, Borrow Clothes, Tell You When Your Hair Doesn't Look Good, Always Fight but Never Drawn Apart, Love You Always, Encorage You When You Are Dawn...*
_A Small Quote For My Sister Love You Always Ameenah😍_
*NO 13*
A rayuwar Jalila indai tana gaban Goggo jinta takeyi kamar yarinyar goye, shiyasa duk wata tabata da shirme juyema Goggo takeyi, suna kwance zasuyi bacci duk ta isheta da neman sanin asalin labarinta.
Goggo tace "to ya isheni haka nan yanzu sai ki kwanta ko kin manta gobe kunada taro a makaranta?"
Jalila ta juyo inda Goggo take tace "Goggo kinsan yanzu addu'ar da nake yi yanzu?"
Goggo tace "ya wuce shirmen soyayyarki?"
Jalila ta girgiza kai tace "A'a addu'a nake Allah ya kara miki lafiya da tsawan kwana muyi rayuwa tare, banaji zan iya kwana d'aya a duniya in bakyanan."
Goggo ta hade rai tace "Jalila nikam sai yaushe ne zaki girma? Na dauka in mutum ya tashi cikin wahala yana hankali amma wani sa'in in kikai wani abun sai inta mamakin ki."
Jalila tai murmushi tace "Goggo a koda yaushe in ina tare dake ji na nake kamar yarinyar goye, kece kawata, mahaifiyata, mahaifina, sannan kuma yar uwata, Goggo yanda bana boye miki komai dan Allah kema kidinga sanar dani komai na rayuwarki."
Kallan tausayawa ta mata dan tabbas tana ji a jikinta wani babban ciwo na cinta domin wasu sababbin canjin da take fuskata a jikinta tasan da matsala,, sai dai fatan Allah yasa abin ba babba bane.
Jalila tace "Goggo!"
Goggo tace "shikenan Jalila na miki alkawari a daren gobe zan sanar dake komai na kafin a haifeki, yanzu dai ki kwanta."
Tace "yauwa Goggona, saida safe."
Goggo ta daga kai, sannan ta zuba mata ido, kankace me Jalila ta tafi bacci.
Goggo a dade tana kallanta har batasan sanda hawaye suka gangaro mata ba, hannu tasa ta share sannan ta gyara mata bargo ta juya ta fara bacci.
Da safe bayan ta gama gyara bangarensu ta fada wanka, an dade ana saba jiki kai kace fatar tata zata canza, ta fito ta bude drawer dinta ta saka kayan makaranta sannan ta shiga duba sababbin dinkin da aka mata, nan ta zabi wani lace mai an karan kyau yasha duwatsu, ta fara kokarin sawa a jakar hannunta da aka sai mata.
Goggo ta bude labule tana kokarin shigowa, kallan Jalila tai tace "ke da zaki makaranta me zakiyi da kayan gida?"
Ta karasa shigowa da kyar ta samu ta zauna.
Jalila tai murmushi tace "Goggo yau fa ake yaye mu."
Tace "to sai akai ya?"
Jalila tace "Ana gama taran ai zamu kwabe mu shiga kayan gida ai shagali."
Goggo ta tabe baki cikin rashin gamsuwa tace " Wai yaushe aka fara haka a makarantar Gomnati ma?"
Jalila tai dariya tace " ina kike