i tauye hakki Ummy, na farko Yaya ba mahaukaci bane, ba kuma nakasashe bane, sannan a zamanin da ai mace ma ance ba sanin wanda zata aura take ba har sai anyi mata auren."
Kallansa tai tace " hakane nima dan Abbanku sai da aka gama komai na ganshi."
Tana fada tana dariya.
Yace "kinji ma ko? Wow Ummy harna kosa naga yarinyar, tunda ta kwanta miki ma tabbatar yarinyar ta gaske ce."
Ummy tace "kai sai yaushe zaka nunamin taka budurwar?"
Yace "nan gaba kadan nafisan ne sai mun rabu ta gama makaranta sai na fara zuwa gidansu a matsayin saurayinta ba malami ba, kinga sai na kawo miki ita kiganta."
Ummy tai murmushi tace "babban burina a duniyarnan bai wuce abubuwa uku ba Sagir, na farko naga yayanka ya warke ya dawo kamar da, na biyu naga ya samu macen da zata kula dashi na uku kuma na ganka kaima da matar da kakeso kuna rayuwar farin ciki."
Sagir yai murmushin jin dadi yace "insha Allah Ummy duka burikan nan naki zasu cika ba da dadewa ba."
Haka suka sauko kasa suna hira.
*****
Kansa yaji yamai gingirin gim, gaba daya dakin yamai zafi, mikewa yai ya fito daga d'akin ya sauko kasa.
Yana jin muryar Ummy dasu Ameera a kitchen, waje yai ya fada motarsa yai waje...........
Wani irin farinciki kwanan nan takeji, ga gida yanzu ana santa sosai, ga tsananin soyayya dake kara shiga tsakaninta da Sagir, jiya suka gama waec zasu fara neco, shine yau ta fita da kanta ta hau mota tace gidansu Zarah ta amso aran wasu litattafanta.
Tana zaune cikin adaidaita tana murmushi suka dan tsaya saboda dan karamin go slow dake gun, gefenta ta kalla motarsa ce a gun, kallan motar tai sannan tai dan tsaki tace " irin motar wannan dan iskan."
Kallan motar ta sakeyi sannan, da yake motar mai tint ce sannan bata ganshi ba a wancan ranar shiyasa bazata iya ganewa ba.
Sa'a akai ya juyo da fuskarsa inda take, kawai ya hangota tana murguda baki da hararar motar, mamaki ya kamashi dan ya tabbatar bata ganinsa bare tace wani abin ya mata.
Har ya dauke idanunsa sai ya kara juyawa, baki ta kara tabewa sannan ta juya kanta tana yan guna guni, kai ya girgiza sannan ya juya fuskarsa.
Jalila tana dan masifa tana cewa ai indai na kama mutumin nan ko ban mai komai ba sai na harareshi irin taimakon nan ma bai iya ba, ba kunya ranar ya mata rashin mutunci.
Hassan kam gaba yai ya tafi can inda ya saba zama, ya kashe motar sannan ya kwantar da kansa a jikin kujera tare da kunna karatun al-qur'ani, kira'ar Malam Abdullahi Abba ne ya zagaye cikin motar.
Jalila an samu jin dadi, yanzu kayanta kala kala, sannan haka zata zauna wani sa'in a falo itafa Yasmeen suyi ta kallansu, duk sanda suke kallan india in ana soyayya itada Sagir dinta kawai take hangowa, ba shakka bata san sanda san Sagir yai nisa a zuciyarta ba.
Goggo najin dadin yanda Jalila yanzu ta murmure duk da ba kiba tai ba amma inka ganta zakaga ba wahala a jikinta.
A kasan zuciyar Goggo har yau hankalinta ya kasa kwanciya da yanda su Mumy da Dady ke jan Jalila a jiki, sai dai duk sanda Goggo ta nemi Jalila data rage zuwa gunsu Jalila sai tace "Goggo Allah ba abinda sukemin sai mutunci."
Jalila an dage sosai ana ta karatun Neco saboda Sagir yace tai karatu sosai dan yanasan yaga matarsa ta cigaba da karatu.
Duk sanda yai wannan maganar sai Jalila ta sunkuyar da kai wai ita kunya, sai dai a kasan ranta wani dadi take ji.
Goggo har ta gaji da labarin Sagir dan kusan kullum sai ta mata tadin shi.
Su kuwa a bangaren su Inner company ya kara habaka saboda sun samu kudi sosai a gun Taura, yanzu company din ma yafi da karfi.
Su uku suke tsara abin biki dan har kayan daki sun fara siya, Safeena kuma suna ta shirye shiryen kaita Egypt wai ta cigaba da karatunta.
Sai dai ni nasan suna kokarin fita da ita ne dan karma a san da zamanta har sai anyi auren.
A can gidan su Ummy kuwa, suma ita da Ameera da Aina'u suna zuwa siyayyar kayan lefe, sanda Aunty nana taji zancen nan har gida tazo tacema Ummy wai tayi dabara ai gwara da suka nemarmai mata ta kudi wai sai yafi daraja.
Sanda tai maganar nan Ummy bata tanka ba dan haryau kalaman Aunty Nana na mata ciwo.
Yau suke zane paper karshe ta neco, suna fitowa suka hau ihon gama makaranta.
Jalila ma zaune itada Zarah a can gefe, Zarah tace "Jalila ni tun jiya nakesan fada miki wani abu."
Jalila tace "menene? Fada kukai da Nasir?"
Zarah ta juyo saitin Jalila sosai tace "Jalila tsoron abinda na aikata nakeyi."
Jalila ta mata kallan tuhuma.
Zarah tace "Jalila jiya Nasir ya sani yin abinda na ke ta tsoro."
Jalila tace " me ya saki yi?"
Idanun Zarah ne suka canza suka ciciko da kwalla tace "Jalila jiya muna tare da Nasir kinsan in zaizo kasan layinmu yake tsayawa sai ni kuma naje saboda tsoron kar yayana ya ganmu, jiya sai na ganshi a mota sai yake cemin motar babansa ce aka aikeshi, bayan mun gama hirarmu a cikin mota zai tafi sai cemin yai wai sai na mai kiss."
Jalila cikin tsantsar mamaki tace "kiss?"
Zarah ta runtse ido cik