and perfect writer's_💡)
*NO 9*
Taura yayi shiru a d’aki yana nazari, Ummy ce ta turo kofar tare da sallama.
Bai jita ba dan ya nustu sosai, kusa dashi ta tsaya tace “Lafiya?”
Kallanta yai sannan yadan murmusa yace “ tsi wlh hankalina ya tafi tunani ne.”
Tace “abinda kajeyi bai yiwu bane?”
Yace “Hafsa dan zauna.”
Zama tai kusa dashi tana kallansa, yace “ yau naga wata yarinya a gidan danaje, ban san meyasa ba naji yarinyar ta kwantamin sosai wanda nakema Hassan sha’awarta, tarbiyarta yasa nake tunanin zata kula da shi fiye da tunanin mu.”
Ummy tace “ yarinyar gidan dakaje ne?”
Yace “eh.”
Zata sake magana Ameera ta bude kofar da gudu tace “Ummy yaya ne.......”
Da gudu suka mike suka hau sama, yana kwance a kasa da alama fadowa ma yai ya kankame jikinsa yasa hannunsa a yuwansa wanda ya kasa jan numfashi.
Sagir sai kokari yake gun taimaka mai, Ummy kasa karasawa tai sai kuka da take yi, Abba ya karasa da sauki yana danna mai kirjinsa, Aina’u da Ameera sai kuka sukeyi.
Da kyar ya ja wani dogon numfashi sannan ya kallesu cikin takaicin halin da yake sa su.
Wasu zafafun hawaye ne suka zubomai yana kallan mahaifiyarsa.
Ummy jiki a sanyaye ta karaso inda yake ta rike hannunsa tace “Hassan!”
Bakinsa ne ya shiga rawa, a hankali yace “Ummy kiyi hakuri.”
Kai ta shiga girgizawa tana kuka tace “Hassan please kadaina fadar haka.”
Sagir ma jiyai hawaye ya zubo masa saboda tausayi, Abba ya sa hannu ya d’agata yace “ ku je ku barshi ya huta.”
Haka suka fito daga d’akin hankalinsu a tashe, Abba ya zauna kusa dashi yace “Hassan meyasa kake kokarin jefa rayuwarka cikin halaka? Sau nawa zamu sanar dakai abinda ya faru a baya ba laifinka bane?dan Allah ka taimakemu ka cirema zuciyarka wannan zargin da takeyi.”
Hassan ya juya kansa gefe kawai baice komai ba, Abba ya mike ya fita, tabbas ya yarda da maganar likita aure ne ya dace dashi, yanzu in tsakar dare ne abin nan ya faru ba wanda zai kula dashi me zai faru?
Ummy kam kuka tai tayi, Sagir yana zaune a kasanta ya rasa ta ina zai fara lallashinta, gaba d’aya gidan a wannan rana ba wanda yai walwala.
***********
Yau da daddare Abba ya gama yanke hukuncinsa dan a daren jiya bacci kalilan yai.
Yau da safe kuwa karfe 10 ya kira wayar Inna.
Bayan sun gaisa ne yace “Hajiya nayi dogon nazari akan al’amarin nan, sai dai ina tunanin haduwa ya kamata muyi ko in sanar dake ta nan?”
Inna tace “Taura duk yanda ka gani.”
Yai shiru kafin yace “Bari in sanar dake ta nan in yaso in kikai tunani sai mu hadu dan yanke hukunci.”
Tace “ba laifi hakan yayi.”
Sai daya danyi shiru kadan kafin yace “ me zai hana muyi yar hadin gida.”
“Yar hadin gida?kamar ya kenan?”
Yace “eh, ina nemawa d’ana babba auran babbar jikarkarki.”
Mikewa tai daga zaman da take tama kasa cewa komai, yace “Hello!”
Tace “ Taura naji, ba matsala mayi magana daga baya.”
Ta katse wayar hankalinta a tashe.
Da sauri ta danna number Dady.
Yana kwance akan gado Mumy ba kwance a kafadarsa suna hira.
Yana ganin wayar Inna ya mike tsaye yace “plm ce.”
Mumy ta turo baki tace “share ta kawai, na tabbatar maganar aiki......”
Bata karasa abinda zata fada ba taji yana cewa “To.”
Yana kashewa taga ya kalleta yace “Inna na neman mu.”
Mikewa tai suka hau sama.
Jalila na ta aiki sanda ta gansu sun hau sama, sun nutsu dan yanda suka ganta alamar ba lafiya.
Inna ta dade kafin ta kallesu tace “Taura ya kirani.”
Mumy tace “ya amince?”
Tace “eh.”
Mumy tace “lalai mutumin nan yanada kudi, wannan uban kudi da muka nema?”
Inna ta mata kallan batada hankali, sannan ta daga waya ta kira Sani a gabansu ta sa a hands free.
Bayan sun gaisa tace “ Sani me kacemin dangane da babban dan Taura?”
Sani yace “ bashida cikakiyar lafiya, dan akwai wanda yacemin ma kwakwalwarsa ba daidai take ba.”
Inna tace to nagode.
Ta kashe wayar sannan ta kallesu tace “hadin aure Taura yake neman yi damu.”
Mumy cikin halin ko in kula tace “Hadin aure da wa kenan?”
Dady kallan Inna yai cikin mamaki, Inna tace “me yasa bakya amfani da kwakwalwarki ne?”
Tace “to ai ni bangane da wa za’ai hadin aure...... “
Dady ne yai saurin tabata sannan ya kalli Inna yace “amma ai baiga Safeena ba.”
Tace “nima abinda ya ban mamaki kenan daga farko, sai daga baya nai tunanin yaransa ashe fa ancemin ba hankali gareshi ba, kaga kuwa ta ya ya zai damu da sai ya ganta? Tunda shine dai kawai burinsa yaga ya sa marmai mata ne?”
Mumy tace “hauka kenan, ta ya ya dan zai bamu kudi zai nemi hadin aure tsakanin mai hankali da mahaukaci?”
Dady ma yace “gaskiya Inna nima ban amince abama Safeena mahaukaci ba.”
Inna tace “me kuke tunani? Kuna tunanin nima a san raina ne?”
Mumy zatai magana sukaji an kwankwasa kofa.
Inna tace “waye?”
Jalila tace “nice, abinci na kawo.”