e ta layin a cikin adaidaita sahu ta dawo daga dan karamin aikin data samu a company din inna, dan bayan rasuwar inna daga filin da Inna ta bar musu da shares din duk kudin sun kare, saboda batsan yanda zata juya su ba, sai da Allah ya taimaketa da Goggo zatai aure Ummy ta tausaya musu, yanzu kam suna cancanawa dan aikin ba wani babba bane dan bata san abubuwa dayawa ba, tadaiyi karatun ne.
Tsaida mai adaidaitar tai ta fita da sauri, yana zaune a bakin masallaci yana alwala, daga dan nesa kadan ta kura mai ido,meya sameshi? Dab taga duk ya canza, juyawa tai ta tsaya idanunta duk sun ciciko, taku uku tai taji ance "Fatima!"
Tsayawa tai cak ta kasa juyawa, yace "ashe dagaske kece? Nayi zatan gizo kika min."
Yanzu kam ta daure ta juyo ta kalleshi, ido suka kurama juna ta daure ta dauke idanunta dan inta tuno abinda ya mata ji take ta tsaneshi gaba daya, juyawa tai kawai ta fara tafiya.
Da gudu yazo yasha gabanta yace "Fatima!"
Karabin dayar hanyar tai tawuce, tai sa'a mai adaidaita ya taho tagun kawai ta tsayar da sauri ta shige.
Shima a hanzarce yaga wani awai ya tsayar yace "dan bimin adaidaitarcan dan Allah."
Nan ya bi bayan su, da yake dama ta kusa zuwa gida bata dade ba ta sauka, zata biya kudi kawai taganshi ya fito, batai mamaki ba sai dai tayi saurin bada kudin da neman juyawa, Yasmeen ce ta leko ta gate din tana ganin itace ta taho da gudu tana murna.
Mumy ta rumgumeta tace "wayace adinga lekowa."
Zata bata amsa ta hango Dady, Yasmeen ta kalleshi cikin mamaki tace "Dady?"
Dan kwanakin ba kadan ba, Dady wanda idanunsa suka ciciko ya tako a hankali ya bude hannayensa, rugawa tai da gudu inda yake ta rungumeshi tace "Dady sai yau ka dawo daga tafiyar? Ta fada tana kuka."
Gaba daya jikinsa ne yai sanyi hawaye suka zubomai, kenan shi da daya koresu ina yake sa ran su zauna? Mikewa yai ya dauketa yace "Yasmeen angirma."
Sannan ya kalli Mumy wacce ta wuce ciki, Tsayawa yai yana kallan gate din gidan, Yasmeen tace "dady muje."
Haka suka shiga cikin gidan Safeena na shara sai ga Mumy tana shigowa ta wuce daki, Safeena zatai magana ta hango dady da Yasmeen.
Gaba daya yanayin fuskarta ne ya canza, Dady ya kalleta yacee "Safeena?"
Dakyar ya lalabata ta shiga ta kiramai Sultan wanda yana fitowa yaga shine ya koma ciki yasa key.
Mumy ma dakyar Safeena tasata ta fito, Dady kam tana fitowa ya sulale ya tsugunna a gabanta, kallansa tai da sauri, Safeena ma ta kalleshi tace "Dady!"
Idanunsa na zubar da hawaye yace "ki yafemin Fatima, ita kadai ce kalmar dazan iya fada miki."
Mumy tai shiru tana kallan yanda yake zubar da hawaye.
Kallansa tai tace "ka tashi mayi maganar."
Yace "ban isa tashi ba harsai kin yafemin."
Mumy tai shiru tana kallansa, tace "gidan ka fa? Naga ka koma haka?"
Nan ya sanar da ita yanda aka kwacemai gidan da komawarsa kauye."
Tausayinsa ne ya kamata dan tana masifar sanshi, abinda ya mata ne yasa ta tsaneshi.
Tai shiru kafin tace "ta yafemai."
Dady yace "nagode."
Na dawo daga baya lokacin da Sultan ya huce."
Ya mike zai tafi, kasa jurewa tai tace " a ina kake kwana?"
Juyowa yai ya kalleta yace "inda ya samu, masallaci ko..." sai kuma yai shiru ganin Safeena na kallansa cikin tausayawa.
Mumy ta juya baya tace "inzaka iya sai ka dinga kwana a falo, kafin ka samu abinyi, sannan in rana tayi sai ka fita.
Kallanta yai kamar yace a'a saboda kunya sai dai inyace ina zai zauna? Yana shirin magana yaga ta shige ciki.
Idanunsa ya runtse dan yasan bai kyauta ba a rayuwarsa.
***********
Yana fitowa daga gidan yaje ya dauko jakarsa sannan ya wuce gidansu Jalila, dan har ya fito zai taho dazu Safeena ta biyoshi gate, ya tsaya yana kallanta, kafin yace "Safeena ki yafemin dan gaba dayanku na cutar daku."
Nine silar dayasa duk abinda ya faru daku ya faru.
Tace "bakomai Dady dukanmu munyi laifi,
sannan bamu bane ya kamata ka fara neman yafiya a gunsu ba, Goggo da Jalila ya kamata ka fara nema."
Yace "Safeena na sani sai dai bansan inda zan samesu ba, ita Jalila ance batanan...."
Da sauri ta katseshi tace "ta dawo, ana bikin kanin mijinta."
Da sauri Dady yace "haba? Bari naje."
Bai jira mai zata ce ba yai waje da sauri, Safeena tai murmushi tace ban fadama Goggo tayi aure ba.
*********
Mika tai tare da yin juye, Hassan ta gani tsaye a kanta.
Idanu ta zare sannan ta mike tace "Yaya?"
Rufto da kansa yai kanta ya sumbaci bakinta, yace "Hajiya Baby kin farka?"
Tace "Yaya yaushe ka tashi? Naga ina rigakafa tashi."
Ya kalleta sannan ya danna wayarsa hasken agoggo ya bayyana, da sauri ta mike zaune tace "11? Inalilahi da alama bana cikin hayacina, ko yaya?ko duk gajiyar bikin ne?
Ya zauna kusa da ita tare da dan sa kansa kadan saman cikinta yace "ya zakiyi? Twins sun sa kin makara?"
Hannu tasa tadan ture kansa daga cikinta tace "yaya da gaske Twins ne?"
Yai ajiyar zuciya yace " maganar gaskiya Jalila banaso na tsorata kine amma