sai dai ke yanzu kinyi gaba, tunda Allah ya dagaki."
Goggo tai murmushi tare da cewa "Ummy Dr ba karamin kyautatamin yakeyi ba, 'ya'yansa ma basida hayaniya, sai godiyar Allah, duk abinda nakeso kafin ma in nema yamin, sannan kinga akwai gidansa na haya da ya barmin, mezan nema nikuwa yanzu a duniyarnan, inba kuma san zuciya nake neman bi ba?"
Ummy ta jinjina kai tace "Alhamdulila ala kulli hal, hakurinki me ya biya miki, Allah ya dubi zuciyarki ne."
Goggo tai dariya sannan tace "Ai duk haduwata da ku shine ya ja min haka, daga ni har Jalila,/ shiyasa akoda yaushe nake gode ma Allah daya hadanu daku."
A tare sukai murmushi.
Lantana ce ta shigo da kaya da sauri ta ajiye tamatso gun Goggo tace "Goggo gashi, kiranki akai."
Goggo ta amsa tare da fitowa daga kitchen din dan tasan Dr ne.
*************
Juye yake akan gado yana ta zuba waya sam bai kula yazo karshen gadon ba, Maimuna tace "nikam kunya nake ji."
Yace "Kunya ko? Ki jira......."
Dim ya tiko daga kan gadon, Maimuna tasa dariya, yace "wayyo Allah na." Dan kam Sageer yaji zafin faduwar, budar kofar Ameera tai dauke da kayan guga, kallansa tai a kasa yana shoshe soshe, dariya ta saka ganin alamar waya yakeyi tace "Yaya anji jiki, ka fito za'a tafi airport."
Ta ajiye kayan ta fita.
******^^^*
Ya dage sosai yanata wanke dakin, sai daya gama tass ya fita sosai sannan ya maida katifar ya shifida ya zauna akai tare dasa kansa a cikin cinyoyinsa yana tunanin rayuwa, tunda ya dawo kauyen nasu mahaifinsa ke kwance ba lafiya, haka ya shiga jinyarsa, baya iya komai sannan komai a kwance yakeyi, haka yai ta kula dashi har Allah ya dau ransa a daren jiya.
Gaba daya rayuwa tamai zafi, yai shiru yanzu shikam baisan ina zai nufa ba dan yan uwansa duk ba wanda yake sanshi, kowa kyararsa yakeyi, yau ya samu ma su barshi ya zauna a waje gun amsar gaisuwa sun hana sun koroshi ciki.
Jakarsa ya dauka dan baiga amfani zamansa ba, dan dama sun sanar dashi mai tarar mai fada wato mahaifinsu ya rasu ya tattara nasa ya nasa ya bar musu gida.
Haka ya fito yana neman zama a tabirmar yayansa yasa kafa agun yace "malam kama gabanka."
Dady ya fito daga kauyen gaba daya abin duniya ya dameshi, balle waccen watan daya wuce yana garin Goggo tazo itada mijinta, haka tazo da kaya kala kala taita rabawa, yanaji zatazo gidansu yabar gidan, haka ta kawo kaya dayawa, haka ya tsaya ta bayan gari yana lekensu.
(Ranar kam ko ni sai da dady yaban tausayi.....lol)
***********
Gida ya cika sosai anata hira da dariya abin gwanin ban sha'awa kana ganinsu kaga mutanen dake cikin farinciki.
Jalila na kankame da Goggonta, Ummy ta kalli Hassan yace "nikam Hassan sai naga Jalila ta rame, ko Goggo?"
Goggo ta kalleta tace "bangani ba nikam."
Hassan yai dariya yace "wato Ummy so kike kice banaba 'yarki abinci ko?"
Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila? Anya ana kila dake kuwa?"
Jalila tai dariya tana kallan Hassan, yana kallanta yace "da alama zuciya zatai kafin Sageer yai aure tana so ta maidani babba saboda kar a rainani."
Ummy tace "babba? Oh Hassan kaikam dai......"
Sai kuma ta tsaya tare da kallansa da sauri tace "Jalila ciki ne da ita?"
Da sauri Jalila ta kalleshi tana mai alamar yai shoru.
Ya kalli Abba yace "Abba ya ka gani na kusa zama baba fa."
Nan fa murna ta karu, Sageer yace "gaskiya ne yaya."
Hassan yai dariya yace "ya? A ina zaka zaunane?"
Yace kasan layin nan, muka samu gida."
Hassan yasa dariya tare da dafashi ya matso kusa dashi yace "wato ni kakesan yima wayau ko? Inyi ta zama anan kenan ko?"
Sageer shima cikin rada yace "ai naji fadanka ne."
A tare sukai dariya Abba yace "ai da kun daina rada dan nikam ina jinku."
Dariya sukai su duka.......
Jalila ce ta kalli Goggo bayan sun shiga dakin Ameera tace "Goggo kinganki kuwa?"
Goggo ta harareta tace "bansan gulma fa, bari na kira Dr yanata san ku gaisa."
Tai murmushi tace " Goggo ya labarin Dady?"
Goggo ta kalleta tace "ina zan sani?"
Jalila tai shiru kafin tace "Yaran sa fa? Duk kuna zaune lafiya?"
Goggo tace "sosai Jalila, har mamaki nakeyi, a farkon auranmu basu saki jiki dani ba saboda ziga na yan uwan mahaifiyarsu, amma daga baya abin kam har mamaki yake bani."
Jalila tai murmushin jin dadi tace "ai gashinan na gani a jikinki."
Haka sukai ta yan hira kafin su fito dan Goggo zata koma gida sai kuma wani satin in za'ai bikin Sageer.
*********
#OneLove๐
[1/11, 10:23 PM] El-hajj: ๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
_Last Page๐_
An daura auran Sageer da Maimuna sun tare a gidansu dake karshen layin su Ummy, gidan ba babba bane sosai sai dai ya tsaru iya tsaruwa.
Ansha shagali kala kala, amarya ta tare a gidanta.
Mumy kam dasu Safeena komawa sukai 'Yan kallo dan yanda Goggo da Jalila suka saje a cikin manyan masu kudi, gaba daya ji sukai bikin yafi karfinsu.
********
Har ta wuc