ko zaka kula da patient?"
Ghali yasa dariya dan ya gane sannan yace "batada aurene?"
Abba yace "tanadashi kuma batadashi."
Cikin mamaki yace "kamar ya?"
Abba yace zan baka labari inmunje gida, dan su Hassan na tafiya gidana zaka musha hira, itama can zata kaga sai ka kara ganinta dakyau."
Ghali yai dariya.
Idanun Jalila gaba daya sun canza, ganin sun fito yin sallama zasu shiga ciki, tana zuwa ta rungume Ummy kawai tasa kuka, Ummy ma idanunta duk suka ciciko, ta shiga shafa bayanta alamar lalashi, Jalila ta dago ta dawo gun Goggo ta rungumeta taba kuka, Goggo kam sai da hawaye suka zubo mata, ta sharesu tare da yi mata addu'a, shikam Hassan yana tsaye gun Abba da Sageer suna magana, kafin Goggo ta dagota tace
"Jalila akara hakuri, karkice akoda yaushe dan mijinki nasanki zan dinga miki duk abinda kikeso, karkizama mai takura masa akan sankanki, sannan ki dinga jin maganar sa, yanzu shine uba, aboki sannan mijinki, kiyi kokafi kyautata masa akoda yaushe."
Jalila ta daga kai tana hawaye, Goggo ta kalli Hassan wanda kentsaye yana jinsu tace "Hassan ga Jalila nan, kawai abinda zance kenan."
Ya kalleta tare da yin murmushi yace "nagane Goggo insha Allah bazan sata kuka mai yawa ba."
Ummy ta makamai harara tace "zaka sata kenan kake cewa?"
Yai dariya yace "eh amma kadan dan haka..." ya fada yana nuna dan karamin yatsansa.
Goggo tai dariya tace "nayarda Hassan."
Jalila ta kalleta sannan ta kalli Ummy tace "Ummy kinjisu?"
Ummy tace "karki damu yana samin ke kuka zanzo in daukeki."
Dariya sukai su dukansu, nan sukama Abba sallama, idanun Jalila ne suka fara neman kara cikowa.
Hassan ya kamo hannunta, da sauri ta kalleshi, yace "in bakyasan na rikike wallahi ki hadiye hawayen nan."
Da sauri ta zare hannunta tare da kokarin hadiye kukanta.
Ya guntse dariyarsa,nan suka karayin sallama da Abba suka wuce ciki.
(Nace a sauka lafiya🕊)
***********
Ghali ne ya kalli Abba yace "inalilahi, ita kuma haka tata kaddarar take?lalai taga bakincikin rayuwa."
Abba yace "ai abin ba'a cewa komai."
Fuskarsa ya shafa sannan yace "amma wannan kwai dan iska, menene laifina dazai wulakantaa haka? Mace kamar ta haka?"
Abba yai shiru cikin takaici.
Yace "to ya shi ya saketa ne?"
Abba ya kalleshi yana dariya yace "kana so ne?"
Yace "naga kai kace in kula da patient ya kake neman canza shawara?"
Abba yai dariya yace "kabar komai a hanuna ni kaina babban burinane maga matarnan na cikin farinciki."
Haka sukai ta hirar Goggo har dare yaja, Ghali yace zai wuce gida.
*********
Zaune yake a kofar gidan sanyi sai ratsashi yakeyi, yanata kiran number Jalila bata shiga, sanyi sai kara kadashi yakeyi ga azabar yunwa dake damunsa, tun safiyar jiya har yau bai ci abinci ba, hasken daya dalleshi ne yasa ya rufe fuskarsa, tsayar da motar yai maimakon ya shiga gidan, ya fito sannan ya kunna fitilar wayarsa yana haska shi.
Dady ya mike da sauri yana neman yin gaba.
Abakar? Abinda ya fada kenan, gaban Dady ya fadi dan yanzu ya gane Abba ne, kasa juyowa yai saboda tsananin kunyar yanda kayan jikinsa da yanda duk ya canza yake.
Abba da sauri ya karaso ya jawoshi, Dady ya juyo tare da yake baki yace "Taura!"
Abba cikin tsananin mamaki yake kallansa yace "menene hakan?"
Ya fada yana kallan jikinsa, Dady ya dan zare hannunsa yace "bakomai."
Abba yace "daga ina kake haka?"
"Daga ina ma zance? Dama zuwa nai ko zanga Jalila inata kiranta bansameta ba."
Abba yace "Jalila ai bata kasar ita da mijinta."
Da sauri Dady ya kalleshi yace "batanan?"
"Suna Kuwait, amma kai meya faru naganka haka? Kwanaki inata nemanka har gidanka naje akacr kum tashi."
Yai shiru yana kallan Abba, Abba yace "Abakar?"
Dady ya kalleshi, idanunsa suka canza yace "dama inasan ganin Jalila ne ta bani dan wasu kudi wanda zan koma kauyen mu dan na gaji da kwana a masallaci ko karkashin gada."
Abba cikin mamaki yace "bangane ba?"
Nan Dady ya sanar dashi abinda ke faruwa, Abba yai shiru yana kallansa kafin yace "Abakar kaga yanda rayuwa take ko? Shiyasa akesan mutum yayi dakyau, yanzu gashinan bakada wani wanda zaka nemi taimako agunsa, bakada wanda zai ji tausayinka, kanada 'ya'ya amma ka banzatar dasu, yanzu meka mora a duniyar nan?"
Dady cikin raunaniyar murya yace "nikam ai banga wani abun dana mora ba...." hawaye suka zobo masa yai saurin gogewa.
Abba ya kalleshi yace "menene matsayin mahaifiyar Jalila a gurinka?"
Kallan Abba yai yace " nikaina ban sani ba."
Abba yamai wani kallo yace "kai kana tunanin da hakkin ta kadai ma zai barka? Ka saketa ne ko me?"
Dady yace "nikaina bansan halin kaina ba, amma ni tun farko ban dauketa a matsayin mata ba."
Abba ya runtsr ido cikin wani irin kunar rai yace "yanzu ba aurenta kenan a kanka?"
Dady da sauri ya kalli Abba, yace "ko akwai?"
Dady yace "bangane nufinka bane."
Abba yace "in ba auranka akanta ka bata takardarta ta nemi miji ta aura, saboda wan