ila da mahaifiyarta, da rashin adalcin dayama Mumy da 'ya'yanta.
Wayarce tai ringing kamar zata katse kafin ya daga, Muryar dady taji akan wai yana waje.
Hassan ya sauko a hankali ya fita waje.
Dady na tsaye a wajen gate, yana ganin Hassan ya taho da sauri, Hassan ya bishi da kalli duk ya wani mole ya canza, kayan jikinsa duk sunyi datti.
Dady ya matso da sauri yace "Ina wuni?"
Cikin mamaki Hassan ya kalleshi yace "Ina wuni?"
Dady ya kalleshi sannan yadan sosa kai yace "Hassan ina Jalilan?"
Hassan ya hade fuska tamau yace "menene dalilin korarmu dakai da mukaje gidanka?"
Dady ha kalleshi jiki a sanyaye sannan yace "Gidan ba nawa bane yanzu."
Hassan ya kalleshi wato tunaninsa ya tabbata, Dady yace "wasu mugaye na hadu dasu suka kwace gidan ba tare da na samu kudina ba."
Hassan ya cigaba da kallansa, Dady ya riko hannunsa yace "Hassan ka taimakeni, wallahi yanzu inda zansa hakarkari na ma bani dashi, Hassan kai mijin 'yatane kantaimaka ka bani ko gida ne inda zan zauna."
Hassan ya bishi da kallo yace "in baka gida? Nidin cema akai gidajen rabarwa gareni?"
Dady yace "nasan na batama dayawa nayima abubuwa kala kala nasan ma gaba daya rayuwata bana kyautawa, sai dai na tuba ka duba ka taimakeni."
Hassan ya zare hannunsa daga nashi yace " da kai a tunaninka hakkin mutanen daka take ka gakesu ne a banza? Ko ka dauka duk abinda kai Allah bazai hukuntaka ba?"
Dady baki na rawa yace "nasan ban kyauta ba."
Hassan yace "zanshiga bacci nakeji dan inada abinyi gobe, harya juya sai kuma ya juyo yasa hannu a aljihu ya zaro wallet dinsa dubu biyar ne a ciki, ya zara ya mikamai, Dady ya amsa satoto yana kallansa, kafin ya tattara abin fada har Hassan ya shige ciki.
Daki ya shiga, ya kwanta kusa da Jalila tare da sa hannu akan fuskarta a hankali yace "am sry Jalila, sai dai ina tunanin barin duniya ta dan gara mahaifinki shine zaisa yasan rayuwa yasan kuma abinda ya aikata bamai kyau bane, kiyi hakuri zan daukeki ba tare da kinsan halin da yake ciki ba, duk lokacin da kika sani zan nemi yafiyarki akan kin taimaka masa danai."
A hankali ya sumbaci bakinta sannan ya kwanta yana kallanta.
********
Dady kam kasa motsawa yai daga kofar gidan, yana tsaye satoto ruke da kudi a hannu, sai dayaji sanyi na busashi sosai sannan ya koma mota ya ja yai gaba gaba daya kansa ya kulle.
Sukam su Jalila washegari suka shirya tsaf, Ummy ta biya itada Abba, Mamman na jansu suka je suka dauko Goggo suka tafi airport.
Sageer kuma da Ameera a gaba Hassan da Jalila a baya, Hassan nata tsokanar Sageer akan budurwarsa, Hassan yace "in bikin yazo ma zo muyi sati daya."
Sageer yace "indai sati ne banaso."
Hassan yana dariya yace "to kwana 10."
Jalila tace "a'a sati biyu dai ya kamata."
Sageer yace "yauwa matar yaya kaga inda ake min kara."
Ameera tasa dariya tace "Gaskiya yaya sati biyu dai."
Ya kalleta yace "wai ni ina Aina'u ne? Sam ta buya"
Ameera tace "Yaya kaida ka gujeta?"
Yace "ba gujeta kamar ya?"
Ta juyo tace "badai yaya bakasani na?"
Jalila ya kalla wacce itama kallansa take, da sauri yasa hannu ya buge kan Ameera yace "to yanzu waya kawo wannan zancen daga tambayarta?"
Ameera tasa dariya tace "Ai naji haushi me makin yaya Sageer ya dan yi mata hucce shine shima ya nemo a waje."
Sageer yace "wa? Ni?"
Haka sukaita zolaya har suka isa airport.
Jalila kam abin kamar mafarki haka take ganninshi wai yau itace zata hau jirgi zuwa wata kasar, abinda takeji a labari.
Goggo ma tayi shiru tana tunanin rayuwa, suna tsaye ne sai ga wani yazo ta gaban Abba, Abba ya kalleshi sannan ya mika mai hannu tare da sakin fuska. Yace "Ghali?"
Wanda ya kira da Ghali ta washe baki yace "kasan tundaga nesa nake kallanka ina zargin ko ba kai bane."
Ghali ya kalli Ummy yace "Hajiya shekaru masu yawa."
Ta kalli Abba tace "wai Dr Ghali naka?"
Yace "nine Hajiya."
Ya kalli Hassan da Sagir yace "'yan biyun ne?"
Ummy tace "eh, ikon Allah."
Ta kalli Hassan tace "kaga wanda yai treating din Yaya (mahaifiyar Hassan) kafin ta rasu."
Hassan ya gaisheshi, su sageer suma suka gaisheshi, Goggo ce ta gaisheshi itama, ya kalleta yace "ka kara aureni?"
Yace "a'a mahaifiyar matar dana ce."
Yace Allah sarki, sun danyi hira kafin sudan ware gefe suna kara tattaunawa, Su Hassan da Jalila kuma suka shiga ciki inda zasu kai kayansu.
Ghali ya kalli inda Goggo take yace "Diabetes's n da ita?"
Abba yace "wa? Ya fada yana kallan gun, ganin Goggo yasa yace "eh wallahi."
Ghali yace "ayya da hawan jini kuma kenan?"
Abba yace "gaskiya ne likita."
Dariya yai kafin Dady yace "ya matarka? Da yaranka?"
Yace "mai dakina Allah ya mata rasuwa shekara biyu da suka wuce yarana kuma sunata karatu, yanzu ma babban ne zai koma makaranta a saudia yakeyi."
Abba yace "Wayyo Allah ya jikanta banji ba ai."
Sannan ya cigaba "Allah ya taimaka kace shi acan yake?
Yace wallahi.
Abba yace "....Ah to